Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade
Published: December 7, 2025 at 4:48 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Wassu ‘yan mata da aka ci zarafinsu ta hanyar yin musu fyade, sun karfafawa gwiwan sauran mata da dukkan wadanda ke fuskantar kuntatawa, su rika fitowa karara suna bayyana matsalarsu ga hukumomi da suak dace, don samun adalci.

A ci gaba da yakin neman kawar da duk wani nau’i na cin zarafi, musamman ma ga mata, a kwanaki goma sha shida da majalisar dinkin duniya ta kebe, kungiyar ‘yan jarida mata, reshen jahar Filato ta gabatar da wassu ‘yan mata biyu ga asibitin kwararru na jahar, don ci gaba da duba lafiyarsu.

Chidimma Augustine wacce aka yi wa fyade, ta kuma sami ciki, da yanzu haka ke wata biyar, tace wanda ya mata fyaden ya ki amincewa, balle ma ya dauki nauyin kaita awu, wanda ya cewarta yace yana bin mahaifinta bashin naira dubu biyar.

Ita ma Justina Dusu wanda tace saurayin ta ne ya mata ciki, bayan ta bayyana masa halin da take ciki, ya rufa tad a bugu da sara da adda har ya fasa mata kwayar ido.

Shugaban kungiyar ‘yan jarida mata, reshen jahar Filato, Madam Grace Akwe Gotip tace kungiyar na bukatar hadin kan al’umma wajen hana cin zarafin mata da taimaka wa wadanda suka fuskanci cin zarafi.

Shima shugaban wata kungiyar matasa dake yaki da cin zarafin al’umma, YIAHVA, Mr Pwakim Jacob Choji, yace tilas sai hukumomi sun aiwatar da dokoki masu tsauri, don kau da cin zarafin al’umma.

Dakta Sa’idu Barnabas, wanda ya karbi ‘yan matan a madadin shugaban asibitin, yace za su yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da ‘yan matan sun sami kulawa mai nagarta.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/CIN-ZARAFIN-MATA.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery
Next Post: Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump Amurka
Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
An Kaddamar Da Jigilar Maniyyata Aikin Hajji A Abuja Afrika
Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wakilan Majalisar Dokokin Phillipines Suna Yunkurin Tsige Shugaban Kasar Afrika
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • Shirin Ga Fili GA Doki Shirye-Shirye
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
  • Gwamnatin Kasar Ghana Ta Rage Farashin Cocoa Afrika
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami Afrika
  • Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.