Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade
Published: December 7, 2025 at 4:48 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Wassu ‘yan mata da aka ci zarafinsu ta hanyar yin musu fyade, sun karfafawa gwiwan sauran mata da dukkan wadanda ke fuskantar kuntatawa, su rika fitowa karara suna bayyana matsalarsu ga hukumomi da suak dace, don samun adalci.

A ci gaba da yakin neman kawar da duk wani nau’i na cin zarafi, musamman ma ga mata, a kwanaki goma sha shida da majalisar dinkin duniya ta kebe, kungiyar ‘yan jarida mata, reshen jahar Filato ta gabatar da wassu ‘yan mata biyu ga asibitin kwararru na jahar, don ci gaba da duba lafiyarsu.

Chidimma Augustine wacce aka yi wa fyade, ta kuma sami ciki, da yanzu haka ke wata biyar, tace wanda ya mata fyaden ya ki amincewa, balle ma ya dauki nauyin kaita awu, wanda ya cewarta yace yana bin mahaifinta bashin naira dubu biyar.

Ita ma Justina Dusu wanda tace saurayin ta ne ya mata ciki, bayan ta bayyana masa halin da take ciki, ya rufa tad a bugu da sara da adda har ya fasa mata kwayar ido.

Shugaban kungiyar ‘yan jarida mata, reshen jahar Filato, Madam Grace Akwe Gotip tace kungiyar na bukatar hadin kan al’umma wajen hana cin zarafin mata da taimaka wa wadanda suka fuskanci cin zarafi.

Shima shugaban wata kungiyar matasa dake yaki da cin zarafin al’umma, YIAHVA, Mr Pwakim Jacob Choji, yace tilas sai hukumomi sun aiwatar da dokoki masu tsauri, don kau da cin zarafin al’umma.

Dakta Sa’idu Barnabas, wanda ya karbi ‘yan matan a madadin shugaban asibitin, yace za su yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da ‘yan matan sun sami kulawa mai nagarta.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/CIN-ZARAFIN-MATA.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery
Next Post: Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
Bayan Rikicin Manoma Da Makiyaya, Kwamitin White Paper Ya Ziyarci Bojude Da Kwami Afrika
An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
Osun: Adeleke Ya Doke Oyebamiji, Ya Ci Gaba Da Rike Kujerar Gwamna Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Kudurin Kasar Ghana Afrika
  • Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
  • Abba Kabir Yusuf Ya Koma Jam’iyar APC Siyasa
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi Afrika
  • Kamfanonin Jiragen Sama Suna Fama Da Karin Farashin Mai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.