Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5
Published: December 9, 2025 at 4:24 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Hukumar kula da rayuwar dabbobi ta majalisar dinkin duniya da masu kare hakkin dabbobi na Afurka sun nuna damuwa ga yanda Jakuna ke matukar raguwa a duniya, saboda kashe su da a ke yi don samun nama da kuma amfani da fatar su wajen magani da ‘yan kasar Sin ke amfani da shi.

A gaba daya duniya alkaluma da aka yi amfani da wata na’ura, na nuni da cewar akwai kimanin Jakuna miliyan 40 a doron kasa.

Lamarin ya ta’azzara bayan ‘yan kasar Sin sun zuba jarin fataucin Jakuna a Najeriya don amfani da fatar Jakin.

Hakan ya haddasa tashin gauron zabi na jakuna da kuma barazanar karar da su har da rahoton shigo da naman bayan sayar da fatar Abuja a soyawa jama’a a matsayin naman yau da kullum.

Tsohon dan majalisar wakilan Najeriya mai sha’awar lamuran kare dabbobi daga cutarwa, Garba Datti Muhammad, ya ce nan da shekara 5 matukar ba a dau matakan da su ka dace ba, Jakuna za su kare a duniya.

Garba Datti wanda ya gabatar da babban jawabi a taron hukumar kula da dabbobi ta majalisar dinkin duniya da ta Afurka, ya ce wasu kan yanka jakuna don amfani da fatar ko cin naman maimakon amfani da jakunan ga lamuran sufuri a karkara.

Datti ya kara da cewa yanzu a duk duniya kimanin Jakuna miliyan 40 a ke da su kuma a na cigaba da hallaka su da cutar da su ba tare da kula da lafiyar su ko gudunmawar da su ke bayarwa ga tattalin arziki ba.

Game da barazanar sayarwa jama’a naman da a ka haramta yankawa na jakuna, wasu manyan makiyaya sun fara tunanin bude mayankar zamani a manyan biranen Najeriya.

Isa Tafida Mafindi tuni ya kafa irin wannn mayankar da ta lashe Naira miliyan dubu goma sha biyar.

Wani abun takaici shi ne yanda mutane ke barin jakuna su hau manyan hanyoyi da dare da kwatsam mai tuka mota sai ya yi kicibis da jaki a tsakiyar titi da kan haddasa mummunan hatsari.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/AS-DONKEYS-SEEM-TO-ON-VERGE-OF-EXTERMINATION-1.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin
Next Post: Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

Iran: Za A Gudanar Da Jana’izar Khamenei Bayan Kwanaki Goma Na Muharram Afrika
Kamfanonin Jiragen Sama Suna Fama Da Karin Farashin Mai Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi Amurka
Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Zargi Kasar Eritrea Da Cin Zarafin Sojojin Habasha Afrika
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
  • Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
  • Yanayin Yunwa Yana Kara Ta’azarra A Somaliya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
  • Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.