Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Sabon Ma’aikacin Tsaro Ne Ya Kashe Amurkawa
Published: December 15, 2025 at 8:43 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mutumin nan da ya kai hari ya kashe Amurkawa uku, sojoji biyu da tafinta daya, a kasar Sham, bai jima da shiga aikin tsaro a kasar ba, inda watanni biyu da suka shige hukumar tsaron cikin gida ta kasar Sham ta dauke shi aiki a zaman mai gadi a wani sansanin soja.

Amma da aka fara damuwa da halayyarsa, sai aka fara zargin cewa yana da alaka da kungiyar ISIS, don haka aka sauya mishi wurin aiki.

Harin da ya kai a kusa da kangon birni mai tarihi na zamanin da, Tadmur, ko Palmyra da turanci, ya kuma raunata wasu mutane 3.

Kakakin ma’aikatar harkokin ckin gida ta Sham, Nour al-Din al Baba, yace dakarun tsaron Sham guda uku ma sun ji rauni a bayan da suka yi musayar wuta da dan bindigar.

Kakakin yace sun fuskanci karancin jami’an tsaro saboda yadda gwamnati ta fado hannunsu haka kwatsam, kuma dan bindigar yana daga cikin mutane dubu 5 da aka dauka cikin wata sabuwar runduna da aka kafa ta tsaron cikin gida.

Amurka

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya
Next Post: Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
Cutar Kurkunu Ta Kusa Zamowa Tarihi A Duniya Amurka
Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa Amurka
Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Kasar Cuba Sunyi Zanga Zanga A Ofishin Jakadancin Amurka Amurka
  • Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
  • Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
  • Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria Siyasa
  • Shugaba Trump Da Gwamnan Minnesota Zasu Sassautawa Bakin Haure Amurka
  • Abba Kabir Yusuf Ya Koma Jam’iyar APC Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.