Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma
Published: December 16, 2025 at 5:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Dokta Nasir Idris, Kauran Gwandu, ya rattaba hannu kan Dokar Kasafin Kuɗi ta shekarar 2026, wadda aka yi wa lakabi da “Kasafin Sauya Fasali da Ƙarfafa Al’umma”, lamarin da ya mayar da kasafin ya zama doka.

An gudanar da bikin sanya hannu a ranar Talata a Fadar Gwamnati da ke Birnin Kebbi, bayan Shugaban Majalisar Dokokin jihar Kebbi, Muhammad Usman Zuru, ya gabatar wa Gwamnan kasafin da Majalisar ta amince da shi.

Kasafin Kuɗin shekarar 2026 ya zo da jimillar kuɗi ₦642,930,818,157.99k, wanda ya haɗa da kuɗaɗen gudanarwa da na manyan ayyuka (recurrent da capital expenditures) domin shekarar kasafin kuɗi ta 2026.

Da yake jawabi, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar, Alhaji Muhammad Usman Zuru, ya bayyana kasafin a matsayin wani muhimmin tarihi da aka cimma sakamakon kyakkyawar haɗin kai tsakanin ɓangaren zantaswa da na majalisa.

Zuru ya bayyana cewa Majalisar ta yi cikakken nazari, muhawara da tantance kasafin bisa tanade-tanaden kundin tsarin mulki da ƙa’idojin majalisa, kafin tura shi ga Gwamna domin amincewa.

Ya ƙara da cewa kasafin kuɗin 2026 ya bayyana hangen nesa na Gwamna Nasir Idris wajen samar da ci gaba mai ɗorewa, bunƙasa ababen more rayuwa, haɓaka ɗan Adam da walwalar al’ummar jihar Kebbi baki ɗaya.

Ya kuma jaddada cewa kyakkyawar fahimta tsakanin ɓangarorin biyu ta sanya jihar Kebbi ta zama abin koyi wajen kula da kuɗin gwamnati da shugabanci nagari.

Shugaban Majalisar ya kuma bayyana cewa cikin shekaru biyu kacal a wannan gwamnati, Majalisa ta 10 ta amince da dokoki 60, dukkaninsu kuma sun samu rattaba hannun Gwamna wani abin alfahari da ba a taɓa samun irinsa ba, wanda ke nuna girmamawar Gwamna ga dimokuraɗiyya da jajircewarsa wajen aiwatar da sauye-sauye.

Ya tabbatar da cikakken goyon bayan Majalisar ga manufofin ci gaban gwamnatin.

A nasa jawabin, Gwamna Nasir Idris ya nuna matuƙar godiya ga Shugaban Majalisar, da shugabannin majalisa da dukkan mambobinta bisa jajircewa, kishin ƙasa da mayar da hankali kan muradun al’umma wajen yin dokoki.

Gwamnan ya bayyana Majalisar a matsayin “Gidan Gaskiya na Al’umma”, yana mai cewa tsauraran matakan da Majalisar ke ɗauka wajen duba shawarwarin gwamnati na ƙara inganta shugabanci tare da tabbatar da cewa dokoki da manufofi sun dace da muradun al’ummar Jihar Kebbi.

Ya jaddada cewa gwamnatinsa ta yi aiki cikin cikakkiyar fahimta da Majalisa ba tare da rikici ba, yana mai cewa shugabanci haɗin kai ne, ba fafatawa ba, domin hidimar al’umma gaba ɗaya.

Gwamna Idris ya kuma nuna muhimmancin ƙara hanyoyin tara kuɗaɗen shiga na cikin gida (IGR), yana mai cewa nasarar aiwatar da kasafin 2026 na dogaro da inganta kudaden Shiga domin ƙara wa tallafin tarayya, wanda bai wadatar da bukatun ci gaban jihar ba.

Ya tabbatar da cewa kasafin ya fi ba da fifiko ga ayyukan da suka shafi al’umma kai tsaye, ƙarfafa matasa, bunƙasa ababen more rayuwa da inganta ayyukan gwamnati, tare da yin sassauci a inda ya dace domin samun fa’ida mafi girma ga jama’a.

A ƙarshe, Gwamnan ya jaddada jajircewar gwamnatinsa ga al’ummar Jihar Kebbi, tare da nuna kyakkyawan fata cewa haɗin kai tsakanin ɓangaren zangltaswa, majalisa da shari’a zai ƙara ƙarfi a 2026, wanda zai hanzarta ci gaba da samar da zaman lafiya mai ɗorewa.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya
Next Post: Ganduje: Mun Janye Shirin Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Karin Labarai Masu Alaka

NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza Labarai
Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika
  • Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
  • Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika
  • CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup  Wasanni
  • Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.