Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne
Published: December 16, 2025 at 8:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan sandan kasar Australiya sun ce ‘yan bindiga biyu da ake zargin sun kai harin da ya kashe mutane 15 lokacin wani biki na Yahudawa a Bondi Beach dake birnin Sydney, sun yi tattaki zuwa kasar Philippines kafin harin, kuma da alamun masu kaunar akida irinta ISIS ce.

‘Yan sandan sun fada yau talata cewa Sajid Akram mai shekaru 50 wanda kuma aka kashe a wurin, da dansa Naveed Akram, mai shekaru 24 da haihuwa wanda shi ma aka harba amma yana kwance a asibiti, sun tafi kasar Philippines a watan da ya shige, kuma ana bincike abinda ya kai su.

Jami’an kula da shige da ficen baki na Philippines sun ce mutanen biyu sun je Manila babban birnin kasar suka wuce Davao a kudancin kasar daga ranar 1 zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba da suka baro can, makonni kadan klafin harbe-harben na Bondi.

Uban ya je shi Philippines dauke da Fasfo na kasar Indiya, shi kuma dan da fasfo na Australiya.

Hukumomi suka ce babu wata shaida da ta nuna wata alaka a tsakaninsu da wata kungiyar ta’addanci ko kuma sa mun horo daga ire-iren su.

Wani musulmi magidanci mai suna Ahmed al Ahmed da ake yaba masa a zaman gwarzo a bayan da yayi kukan kura ya abka kan daya daga cikin ‘yan bindigar, sannan yana kwance a asibiti a Sydney yana jinyar harbinsa da aka yi har sau hudu.

Shugabannin Australiya da ma shugaba Donald Trump na Amurka suna yaba ma Ahmed a zaman gwarzo.

Asusun da aka kafa na nema masa gudumawar kudin jinya a yanzu ya tara fiye da Dala miliyan 1 da dubu 260.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya!
Next Post: Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta Amurka
Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Amurkawa Sun Nuna Bacin Rai Saboda Yawaita Kashe ‘Yan Kasar Amurka
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
  • Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
  • Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu Labarai
  • Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.