Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia
Published: December 25, 2025 at 7:33 AM | By: Bala Hassan

Amurka ta sanya hanu kan sabbin yarjejeniyoyin kan kiwon lafiya da kasashen Madagascar, Saliyo, da Botswana, da kuma Ethiopia, wadda adadin kudaden da shirin zai bukata suka kai kusan dala bilyyan 2 da milyan 300, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fada a ranar talata.

A cikin watan Nuwambana bana ne gwamnatin shugaba Trump ta bayyana wani sabon tsarin tallafi gameda tallafin Amurka take bada wa ga kasashen ketare, da ya fi maida hankali wajen ganin kasashen da take taimakawa suna daukan hakkin kula da kiwon lafiyar kasashen su.

A cikin ko wace yarjejeniya ta kunshi sharudda da suka hada da aiwatar da ita sau da kafa, da kuma matakan ladabtarwa idan aka kaucewa yarjejeniyar, auna ci gaba da ake samu wajen ganin bayan barazana daga wasu cututtuka, da kuma kaucewa dogaro kan tallafin  da Amurka take bayarwa, kamar yadda ma’aiktar harkokin wajen Amurka ta fada a cikin wata sanarwa data fitar.

A duka yarjejeniyoyin Amurka ta kuduri anniyar zata kashe kudi dala bilyan daya da milyan dari hudu, yayinda kasashen hudu su  kuma za su kashe dala milyan dari tara daga aljehunansu.

Ofishin jakdancin Amurka dake Abidjan babban birnin kasar Ivory Coast ta ce sanya hanu kan yarjejeniyar kiwon lafiya na tsawon shekaru biyar da kasar, za’a gudanar da shi ranar Alhamis idan Allah ya kai mu.

Kamar yadda ofishin jakadancin ya ci gaba da cewa, yarjejeniyar an tsara ta ne da nufin karfafa hanyoyin gano bullar cututtuka da samar da ma’aikata, ta kara da cewa, Amurka zata samarda kudi dala milyan 273, Ivory coast kuma zata bada kudi bilyan 252 na kudin sefa.

Ahalinda ake ciki kuma, matakin janye jakadu masu yawa daga kasashen Afirka da suke kudu da hamadar sahara da Amurka tayi, zai bar Washington bata da manyan kwararru a kusan rabin kasashe da suke yankin, matakin da zai kara dagula yunkurin aiwatar da burin gwamnatin TRump a yankin da yake fama da juyin mulkin soja.

Tun fara aikin gwamnatin Trump, hukumomi a Washington suka bada karfi wajen gudanr da harkokin kasuwanci maimakon bada karfi kan tallafi.

Shugaba Trump ya maida karfi wajen ganin an cimma zaman lafiya, da kuma sanya hanu kan yarjejeniyin samarda muhmman albarkatun kasa, maimakon tallafi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai
Next Post: Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

Bayan Shafe Shekaru Hudu A Mulki Sarkin Hausawan Ibadan Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Bukaci Sabbin Shugabanni Su Yi Jagoranci Nagari da Inganta Ayyukan Jama’a Labarai
An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Ya Hallaka Mutane Uku A Jihar Yobe Labarai
An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami Tsaro
  • Za’a Saka Tarihin Trump A Manhajar Makarantu Don Jajircewasa Da Kwazo Amurka
  • Rikicin Siyasa A Jihar Rivers Sakamakon Ayyana Fubara A Matsayin Shugaban APC Siyasa
  • Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
  • Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
  • ‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika
  • Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.