Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya
Published: December 26, 2025 at 1:33 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

A bisa rokon hukumomin Najeriya, mayakan Amurka sun kai hare-hare ta sama a kan sansanonin da aka ce na ‘yan kungiyar Daesh, ko ISIS ne, a jihar Sakkwato dake yankin arewa maso yammacin kasar cikin daren nan da ya shige.

Rahoton farko game da wannan harin ya fito ne daga bakin shugaba Donald Trump na Amurka wanda ya ce a bisa umurninsa, Amurka ta kai munanan hare-hare ta sama a kan ‘yan ISIS wadanda a cewarsa su na kashe kiristoci a yankin.

Daga bisani, rundunar sojojin Amurka mai kula da nahiyar Afirka, AFRICOM, ta fito da wata sanarwar dake cewa an kai wannan harin ne bisa rokon hukumomin Najeriya, kuma an kashe ‘yan ISIS da dama.

Ita ma ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, ta fitar da sanarwa dazun nan tana fadin cewa wannan harin da aka kai ya samo asali ne daga yarjejeniyar hadin kan tsaro da musanyar bayanan leke asiri.

Wata sanarwar da mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, ya bayar cikin daren nan, ta tabbatar da cewa lallai Najeriya ce ta bukaci a kai wannan hari kan sansanonin ‘yan ta’addar a karkashin yarjejeniyar hadin kan tsaron da ta kulla da Amurka da nufin shawo kan matsalolin tsaro da suka addabi yankin arewa maso yammacin Najeriya.

Ma’aikatar ta ce gwamnatin Najeriya zata ci gaba da yin aiki da kawayenta ta hanyoyin diflomasiyya da tsaro domin nakkasa ‘yan ta’adda da ayyukansu na ta’addanci a kasar.

A ranar litinin kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ba da labarin ewa tun a cikin watan Nuwamba Amurka ta fara shawagin leken asiri a sassa masu yawa na Najeriya.

Gwamnatin Najeriya ta ce wadannan ‘yan bindiga da kuma ‘yan ta’adda ba su ware addini, suna kai hare-harensu a kan Musulmi da kiruista, kuma ikirarin da Amurka keyi na cewa ana kisan kare dangi ma kirista babu ka mshin gaskiya a cikinsa.

Najeriya ta yarda zata yi aiki da Amurka wajen karfafa yakar wadannan ‘yan ta’adda.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa
Next Post: Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan-Ta’adda Sun Kara Sace Mutane A Jihar Naija! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ECOWAS Zata Kafa Rundunar Yaki Da Rashin Tsaro Afrika
  • An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
  • Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.