Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji
Published: December 27, 2025 at 6:35 PM | By: Bala Hassan

Gwamnati Ta Kammala Horar da Sama da Matasa 7,000 a Matsayin Masu Tsaron Daji Da Za a Tura su Aiki Nan take

Gwamnatin Tarayya ta sanar da kammala horar da fiye da matasa 7,000 da aka dauka a matsayin Masu Tsaron Daji (Forest Guards) a jihohi bakwai da ake ganin suna fuskantar matsanancin barazanar tsaro.

Wannan horo ya gudana ne karkashin shirin Presidential Forest Guards Initiative da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya kaddamar a watan Mayu na shekarar 2025 domin dawo da ikon gwamnati a cikin dazuzzuka da ke kara zama mafakar ‘yan ta’adda, ‘yan fashi da makami da masu garkuwa da mutane.

An gudanar da bikin yaye daliban a ranar 27 ga Disamba, 2025 a jihohi Borno, Sokoto, Yobe, Adamawa, Niger, Kwara da Kebbi, inda kowane bangare na horon ya kasance mai tsauri da tsari, domin gina dakaru masu kwarewa da jajircewa wajen aikin cikin daji da wuraren da ba a iya shiga cikin sauki.

A bayanin da ya gabatar a bikin yaye su, Mai Ba Da Shawara kan Tsaron Kasa, Malam Nuhu Ribadu, ya bayyana shirin a matsayin “mataki mai karfi” wajen dawo da zaman lafiya da kare al’ummomi.

“Wadannan Masu Tsaron Daji ba kawai ma’aikata bane da suka sa kaya. Su ne masu kare al’umma, masu tarin bayanai, kuma ginshiki a cikin tsarin tsaronmu. Za su tsaya a kasa, su wanke wuraren da masu aikata laifi ke buya, su kuma taimaka wa jami’an tsaro wajen kwato yankunan da miyagu suka mamaye,” in ji shi.

Ya kara da cewa, babu wani tazara tsakanin kammala horo da fara aiki:

“Nan da nan za a tura su bakin aiki, albashinsu da hakkokinsu za su fara nan take.”

An shafe watanni uku ana horar da wadanda aka dauka, inda aka mayar da hankali kan:

Horon jiki da kwakwalwa (physical & mental endurance)

Tsallake cikas, da hanyoyin jure doguwar tafiya cikin daji

Horar da su kan dabarun yaki da tsari na tsaro (tactical drills)

Horo kan mayar da martani yayin farmaki, da kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su

Horon kyakkyawar mu’amala da fararen hula, kare hakkin bil’adama, da bin doka

Daga cikin wadanda suka halarta horon, kashi 98.2 cikin ɗari ne suka kammala. An kori mutane 81 sakamakon kin bin ka’ida, yayin da biyu suka rasu saboda matsalolin lafiya. Mafi yawansu ’yan asalin yankunan da za su yi aiki ne, abin da gwamnati ta ce zai taimaka musu wajen sanin daji, hanyoyin shiga da fita, tare da samun goyon bayan al’umma.

Masu Tsaron Dajin na karkashin kulawar Ofishin Mai Bada Shawara kan Tsaron Kasa tare da Ma’aikatar Muhalli, karkashin daidaitawar DSS da Hukumar National Park Service. Haka kuma rundunar soji, rundunar sojin ruwan Najeriya, rundunar ’yan sanda da NSCDC duk sun bayar da gudummawa wajen tsari da dabarun aiki.

Gwamnoni da mataimakansu daga jihohin da abin ya shafa sun halarci taron, ciki har da Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, da Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni, yayin da wasu jihohin suka samu wakilci daga mataimakan gwamnoni.

A karshe NSA Nuhu Ribadu ya sake jaddada kudirin gwamnati na ci gaba da fadada shirin zuwa sauran jihohi:

“Idan muka kare dazukanmu, mun kare kasa. Idan muka kare kasa, mun kare rayukan al’ummanmu. Gwamnatin Tarayya ba za ta yi kasa a gwiwa ba.”

Labarai

Post navigation

Previous Post: Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe
Next Post: Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto

Karin Labarai Masu Alaka

Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
Hukumar Hasashen Kasuwanci Na Zargin Saida Bayanan Sirri Amurka
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najib Razak Zai Kara Shekaru 15 A Gidan Yari Saboda Cin Zarafin Kujerar Mulki Labarai
  • Tashoshin Mai Basa Iya Loda Mai A Rasha Labarai
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • Shugaba Trump Ya Bukaci Kasar Iran Ta Mika Wuya Amurka
  • Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane Labarai
  • Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
  • Isra’ila Ta Kashe Babban Jami’in Tsaron Iran Ali Larjani Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.