Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai
Published: November 16, 2025 at 12:32 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Kasar Iran ta tabbatar a yau Asabar cewa dakarunta na juyin juya hali sun damke wani jirgin tanka da suka ce ya keta dokoki, wanda ke dauke da fetur a cikin tekun Gulf, wanda aka ce ya doshi kasar Singapore.

A jiya jumma’a ne jami’an Amurka da majiyoyin tsaron zirga zirgar jiragen ruwa suka ce dakarun Iran sun tare wannan jirgi suka juya akalarsa zuwa cikin yankin ruwan kasar Iran din.

Wannan shine karon farko da Iran take kama wani jirgin ruwa a cikin tekun Gulf tun cikin watan Afrilun 2024.

Gidan Talebijin na Iran ya karanta wata sanarwar da Rundunar Dakarun Juyin Juya Hali ta kasar ta bayar dake cewa,  jirgin ruwan tankar ya keta doka ta hanyar dauko kayayyakin da ba a amince da safararsu ba. Sanarwar ba ta yi karin bayani a kan wannan abu da ake zargi.

Wannan jirgin ruwan da Iran ta kama a mashigin ruwan Hormuz, ya yi lodi ne a Sharjah dake Hadaddiyar Daular Larabawa.

Iran dai ta dakile yawan ayyukanta na soja a yankin tun bayan dauki ba dadin da suka gwabza da Isra’ila da  Amurka a watan Yunin wannan shekara.

Labarai

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke
Next Post: Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Ghana Ta Bayyana Fataucin Bayi A Matsayin Babban Laifi Afrika
Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
Wani Alkali A Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Kasar Afrika
Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Indiya Da Brazil Sun Kulla Yarjejeniyar Cinikayya Afrika
  • FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • EFCC Ta Cafke Fitacciyar Jarumar Kannywood Samha Inuwa Labarai
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
  • An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.