Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai
Published: November 16, 2025 at 12:32 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Kasar Iran ta tabbatar a yau Asabar cewa dakarunta na juyin juya hali sun damke wani jirgin tanka da suka ce ya keta dokoki, wanda ke dauke da fetur a cikin tekun Gulf, wanda aka ce ya doshi kasar Singapore.

A jiya jumma’a ne jami’an Amurka da majiyoyin tsaron zirga zirgar jiragen ruwa suka ce dakarun Iran sun tare wannan jirgi suka juya akalarsa zuwa cikin yankin ruwan kasar Iran din.

Wannan shine karon farko da Iran take kama wani jirgin ruwa a cikin tekun Gulf tun cikin watan Afrilun 2024.

Gidan Talebijin na Iran ya karanta wata sanarwar da Rundunar Dakarun Juyin Juya Hali ta kasar ta bayar dake cewa,  jirgin ruwan tankar ya keta doka ta hanyar dauko kayayyakin da ba a amince da safararsu ba. Sanarwar ba ta yi karin bayani a kan wannan abu da ake zargi.

Wannan jirgin ruwan da Iran ta kama a mashigin ruwan Hormuz, ya yi lodi ne a Sharjah dake Hadaddiyar Daular Larabawa.

Iran dai ta dakile yawan ayyukanta na soja a yankin tun bayan dauki ba dadin da suka gwabza da Isra’ila da  Amurka a watan Yunin wannan shekara.

Labarai

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke
Next Post: Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka Afrika
An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai
  • Rundunar Sojin KTK Ta Harba Makami Teku Afrika
  • Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
  • Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
  • Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
  • Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.