Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai
Published: November 16, 2025 at 12:32 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Kasar Iran ta tabbatar a yau Asabar cewa dakarunta na juyin juya hali sun damke wani jirgin tanka da suka ce ya keta dokoki, wanda ke dauke da fetur a cikin tekun Gulf, wanda aka ce ya doshi kasar Singapore.

A jiya jumma’a ne jami’an Amurka da majiyoyin tsaron zirga zirgar jiragen ruwa suka ce dakarun Iran sun tare wannan jirgi suka juya akalarsa zuwa cikin yankin ruwan kasar Iran din.

Wannan shine karon farko da Iran take kama wani jirgin ruwa a cikin tekun Gulf tun cikin watan Afrilun 2024.

Gidan Talebijin na Iran ya karanta wata sanarwar da Rundunar Dakarun Juyin Juya Hali ta kasar ta bayar dake cewa,  jirgin ruwan tankar ya keta doka ta hanyar dauko kayayyakin da ba a amince da safararsu ba. Sanarwar ba ta yi karin bayani a kan wannan abu da ake zargi.

Wannan jirgin ruwan da Iran ta kama a mashigin ruwan Hormuz, ya yi lodi ne a Sharjah dake Hadaddiyar Daular Larabawa.

Iran dai ta dakile yawan ayyukanta na soja a yankin tun bayan dauki ba dadin da suka gwabza da Isra’ila da  Amurka a watan Yunin wannan shekara.

Labarai

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke
Next Post: Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci Afrika
Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
Tinubu Ya Jaddada Buƙatar Kare Rayukan ‘Yan Afirka A Taron ECOWAS Afrika
Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
  • Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika
  • An Kama Maharan Bom Din Maiduguri Tsaro
  • Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.