Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna
Published: January 2, 2026 at 12:20 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 2, 2026

Rasha da Ukraine suna zargin juna da auna hare hare kan farar hula a ranar farko ta sabuwar shekara, inda Rasha tayi zargin Ukraine ta kai mummunar hari akan wai O’tel a yankin kudancin kasar data mamaye, yayin da hukumomi a Kyivi suke zargin Rasha ta auna hare hare kan tashoshin makamashin wutan lantarki.

Rahotannin nan suna zuwa ne a dai dai lokacin da aka zafafa yin shawarwari da zummar kawo karshen yakin na kusan shekaru hudu, ko wacce daga cikin kasashen biyu masu gaba da juna, tana zargin dayar da kokarin cewa ra’ayinta ne ya fi samun karbuwa da goyon bayan shugaban Amurka.

“A ranar sabuwar shekara, da-gangan Rasha ta auna Ukraine da hare hare da jiragen drones da basu da matuka cikin dare.”

Shugaba Volodymyr Zelensky ya rubuta a shafin sa dake dandalin Telegram, yana mai cewa a hare haren, Rasha ta auna tashoshin samar da wutan lantarki a yankunan kasar bakwai.

A nata bangaren Rasha ta zargi Ukraine cewa ta kashe akalla mutane 24 ciki har da jariri a wani hari data kai da jiragen drones kan wani O’tel da wurn cin abinci da shakatawa a yayinda mutane suke murnar shigar sabuwar shekara a yankin Ukraine na Kherson dake kudancin kasar.

Sai dai da take magana, rundunar mayakan Ukraine wacce ta sha sukar Rasha a kan kai hare hare kan farar hula, tace hare haren da take kaiwa duka tana auna su ne kan cibiyoyin soja da kuma tashoshin makamashi, amma bata ce komi ba kan zargin kai hari kan O’tel ba.

Shugaba Zelensky yace, harin na Rasha yayinda ake hutun sabuwar shekara, ya nuna cewa Ukraine ba zata iya jurewa jinkiri kan kayan tsaro ta sararin samaniya ba.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi
Next Post: Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu

Karin Labarai Masu Alaka

Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya Labarai
Guguwa Mai Karfi Ta Raunata Dubban Mutane A Madagascar Labarai
An Gudanar Da Jana’izar ’Yan Jaridan Da Suka Rasu A Jihar Gombe Labarai
Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
Najib Razak Zai Kara Shekaru 15 A Gidan Yari Saboda Cin Zarafin Kujerar Mulki Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba Afrika
  • Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu Afrika
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu Tsaro
  • Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
  • Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika
  • Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.