Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC
Published: January 3, 2026 at 9:54 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 4, 2026

Dalilan da su ka sanya sauya shekar Gwamna Abba zuwa APC ya samu tsaiko.

An gano dalilan da suka sa aka dage sauyin sheƙar Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, bayan an riga an kammala shirye-shirye na farko.

A ranar Juma’a, wasu majiyoyi sun rawaito cewa gwamnan ya kammala shirye-shiryen sanar da sauyin jam’iyyarsa zuwa APC a ranar Litinin.

Kafin a dage batun sauyin jam’iyyar, hedikwatar jam’iyyar APC ta ƙasa ta shirya cewa gwamnan zai zama mutum na farko da za a yi wa rajista a Kano a sabon tsarin rajistar yanar gizo na jam’iyyar.

Bisa tsarin da aka fara tsara wa, tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje, ne zai raka gwamnan zuwa mazabarsa ta Diso domin yin rajista a shafin yanar gizon jam’iyyar tare da karɓar katin jam’iyya.

Bayan kammala rajistar gwamnan, an shirya cewa nan take zai raka Ganduje zuwa garinsa na asali a karamar hukumar Dawakin Tofa domin sabunta rajistarsa a sabon shafin yanar gizon jam’iyyar.

Sai dai wasu majiyoyi sun shaidawa DAILY NIGERIAN cewa Shugaba Bola Tinubu ne ya bayar da umarnin a dakatar da sauyin shekar ta Abba har sai an yi ƙoƙari wajen shawo kan uban gidansa na siyasa, Rabiu Kwankwaso.

A cewar majiyoyin, shirin Kwankwaso na sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ADC ya sauya lissafin APC.

“Fadar Shugaban Ƙasa na da bayanan sirri cewa Kwankwaso ya gana da Obasanjo da Peter Obi, kuma akwai yiyuwar su haɗa kai domin kalubalantar Tinubu a 2027 kuma  Tikitin Obi/Kwankwaso haɗin gwiwa ne mai ƙarfi da zai iya sauya ma’aunin siyasar APC.

“Kuma idan babu Kwankwaso, ƙarfin siyasar gwamnan zai ragu, saboda haka Tinubu na sake tunani kan sauyin jam’iyyar Gwamna Yusuf.

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida wa wannan jarida cewa gwamnan da kansa ne ya nemi ƙarin lokaci domin ya samu damar shawo kan ƙarin mambobin Majalisar Dokoki ta Jiha da ta Ƙasa su bi sahunsa wajen sauyin jam’iyyar.

Wasu majiyoyi da ba a tabbatar da su ba sun kuma shaida cewa matsin lambar da gwamnan ke fuskanta ta sanya shi cikin ruɗani, har ta kai ga yana tunanin janye batun sauyin jam’iyyar tare da komawa ya sake haɗewa da uban gidansa Kwankwaso.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico!
Next Post: Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona!

Karin Labarai Masu Alaka

“Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnan Bauchi Ya Shiga Neman Mafita Kan Lalacewar Matatar Ruwan Alkaleri Afrika
Kannywood: Ali Nuhu Ya Shiga Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu Afrika
Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
Sarkin Kagarko Ya Rasu Yana Da Shekaru 110 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gombe Ta Zo Ta Biyu Wajen Aiwatar Da Shirin L-PRES Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya
  • China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
  • CNG Ta Farfado Da Jarin Masu Adaidaita Sahu A Kaduna Afrika
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza Labarai
  • Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
  • Amy Hunt Ta Zama Sabuwar Tauraruwar Wasannin Guje-guje Ta Birtaniya Wasanni
  • Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.