Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa
Published: January 8, 2026 at 7:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Barau Jibrin, ya karyata zargin cewa majalisar dokoki ta ƙasa tana bin umarnin bangaren zartarwa ba tare da ‘yanci ba.

Barau Jibrin ya bayyana hakan ne a Ilorin yayin da yake gabatar da laccar bikin yaye ɗalibai karo na 15 a Jami’ar Al-Hikmah, inda ya ce haɗin kai tsakanin majalisa da bangaren zartarwa an yi shi ne domin samar da kyakkyawan shugabanci.

Ya danganta kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin bangarorin biyu da kwarewar Shugaba Bola Tinubu a matsayin tsohon gwamna kuma ɗan majalisa, yana mai cewa hakan ya ƙarfafa fahimta, sadarwa da shawarwari, musamman wajen gabatar da kudurorin dokoki.

Mataimakin shugaban majalisar dattawan ya ce wasu na kuskuren fassara wannan haɗin kai a matsayin majalisa ta zama “yar amshin shata” kawai, yana mai jaddada cewa haɗin kai ya fi rikici amfani ga ci gaban ƙasa.

Ya ƙara da cewa dorewar dimokuraɗiyya na buƙatar bin kundin tsarin mulki, hikima da wayayyun ‘yan ƙasa masu kishin ƙasa.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi
Next Post: Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa

Karin Labarai Masu Alaka

An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya: Ta Aiwatar Da Tsarin Ba Aiki Ba Albashi Ga Ma’aikata Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai
  • An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
  • Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.