Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa
Published: January 8, 2026 at 7:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Barau Jibrin, ya karyata zargin cewa majalisar dokoki ta ƙasa tana bin umarnin bangaren zartarwa ba tare da ‘yanci ba.

Barau Jibrin ya bayyana hakan ne a Ilorin yayin da yake gabatar da laccar bikin yaye ɗalibai karo na 15 a Jami’ar Al-Hikmah, inda ya ce haɗin kai tsakanin majalisa da bangaren zartarwa an yi shi ne domin samar da kyakkyawan shugabanci.

Ya danganta kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin bangarorin biyu da kwarewar Shugaba Bola Tinubu a matsayin tsohon gwamna kuma ɗan majalisa, yana mai cewa hakan ya ƙarfafa fahimta, sadarwa da shawarwari, musamman wajen gabatar da kudurorin dokoki.

Mataimakin shugaban majalisar dattawan ya ce wasu na kuskuren fassara wannan haɗin kai a matsayin majalisa ta zama “yar amshin shata” kawai, yana mai jaddada cewa haɗin kai ya fi rikici amfani ga ci gaban ƙasa.

Ya ƙara da cewa dorewar dimokuraɗiyya na buƙatar bin kundin tsarin mulki, hikima da wayayyun ‘yan ƙasa masu kishin ƙasa.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi
Next Post: Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa

Karin Labarai Masu Alaka

TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
  • ‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
  • Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika
  • ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
  • Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta Amurka
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.