Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya
Published: January 19, 2026 at 9:08 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumomin tsaron kasar Libya sun kubutar da bakin haure fiye da 200 daga wani kurkukun sirri da aka gina a karkashin kasa a garin Kufra dake yankin kudu maso gabashin kasar, a inda aka tsare su cikin wani mummunan yanayi.

Wasu majiyoyin tsaro biyu a kasar sun ce hukumomi sun gano wannan kurkuku da aka gina mai zurfin mita 3 a karkashin kasa a garin na Kufra wanda wani madugun ‘yan safarar mutane na Libya yake gudanar da shi.

Daya daga cikin majiyoyin yace har yanzu ba a kama mutumin da ya gina yake gudanar da wannan kurkuku na sirri ba.

Majiyar ta ce wasu daga cikin wadannan bakin haure sun shafe shekaru 2 suna daure a ciki. Daya majiyar kuma ta ce sumamen da aka kai ya bankado laifi na cin zarafin bil adama mafi muni da aka taba ganowa a yankin.

Bakin hauren da aka kubutar daga wannan bala’i sun fito ne daga kasashen kudu da hamadar Sahara, kuma akasarinsu daga kasashen Somaliya da Eritrea, kuma sun hada da mata da yara kanana. Garin Kufra yana gabashin Libya, kimanin kilomita 1700 daga Tripoli, babban birnin kasar.

Tun bayan da kungiyar kawancen tsaro ta NATO ta taimaka wa ‘yan tawaye wajen kawarwa da kashe shugaba Muammar Gaddafi a 2011, Libya ta zamo zangon safarar bakin hauren dake tserewa daga yake-yake da talauci, wadanda ke bi ta wannan hanya mai hatsarin gaske ta cikin hamada bisa zummar samun hanyar kaiwa kasashen Turai.

A makon da ya shige ma, an gano gawarwakin bakin haure su 21 a wani ramin da aka haka aka binne su a yankin na gabashin Libya, inda aka samu wasu da suka kubuta da rayukansu da aka ga alamun an gana musu azaba kafin a sake su

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain
Next Post: Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
Jana’izar Jagoran Ƙolin Iran Ta Kawo Tsauraran Matakan Tsaro A Tehran Afrika
Sojojin Amurka Sun Kutsa Cikin Kasar Iran Labarai
Kaduna: Masana Sun Nemi A Sauya Tsohon Wurin Zubar Da Shara Na Tudun-Ilu Afrika
Shugabannin Kiristocin Arewa Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Ummulkhairi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
  • Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta Wasanni
  • Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya Wasanni
  • Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
  • Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas Labarai
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai
  • Matar El-Rufai Ta Roƙi Tinubu Ya Tabbatar An Yi Wa Mijinta Adalci Afrika
  • CNG Ta Farfado Da Jarin Masu Adaidaita Sahu A Kaduna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.