Hare -hare da jiragen drone sun hallaka fararen hula da dama a ciki da wajen al-Obeida da ke kwaryar kasar Sudan, yayin da kazamin yakin basasasar da ake ta fafatawa a kasar ya kara kutso kai cikin birnin da sojoji ke iko, a cewar mazauna wurin.

Al- Obeida ta kasance daya daga cikin muhimman biranen Sudan, kuma babban birnin jihar arewacin Kordofan, wanda yake wani bangare na yankin Kordofan, da Yayi iyaka tsakanin kungiyar ‘yan tawayen RSF da ke da karfi a Darfur da kuma rabin gabashin kasar da sojoji ke rike da iko.
Yaki ya barke a Sudan ne a shekarar 2023, bayan da sojoji da ‘yan kungiyar RSF suka kara da juna a kokarin su na kafa gwamnatin demokradiya. Yakin Yayi sanadiyar jefa kusan rabin al’ummar kasar cikin fatara da yunwa, kuma ya lalata tattalin arzikin ta.
Amfani da jiragen drone domin kai hari, ya dara na sauran makamai, musamman ma ‘yan tawayen RSF na yawan amfani da su don dakile rinjayen da sojoji ke da shi na yakin sama.


