Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo
Published: January 26, 2026 at 8:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu ‘yan kungiyar ‘yan ta’adda da ke da alaka da kungiyar ISIS a gabashin Congo sun hallaka a kalla mutane 25 a cewar masu rajin kare hakki a lardin Ituri.

Wadanda aka kashe sakamakon harin da kungiyar Allied Democratic Forces, wato IDF ta kai, sun hada da maza 15 da aka kone da ran su a wani gida, da wasu 7 da aka harbe a kauyen Apakulu, a yankin Irumu da ke lardin Ituri. Uku kuma an kashe su ne a yankin gudanar da ayyuka na Walese Vonkutu.

Shugaban kungiyar masu rajin kare hakki, Christophe Muyanderu, yace abun ya faru wajajen karfe 4 na asuba, inda rayuka a kalla 25 suka salwanta. Ya kara da cewa wannan hari na ADF kisan gilla ne karara.

Ba’a ji daga kungiyar ta ADF kan lamarin ba.

Jamhuriyar Demokradiyar Congo dai na yawan samun hare-hare a watannin baya bayan nan daga kungiyoyin ‘yan tawaye da suka hada da ADF kuma kungiyar M23 da kasar Rwanda ke marawa baya.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Za’a Gurfanar Da Sojojin Da Ake Zargi Da Yunkurin Juyin Mulki
Next Post: Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine

Karin Labarai Masu Alaka

Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
Nuhu Ribadu Ya Mika Yara 130 Da Aka Kubutar Ga Gwamna Bago Tsaro
Anyi Janazar ‘Yan Shi’a 33 Da Aka Kashe A Masallacin Juma’a Sauran Duniya
Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Wajen Hakar Ma’adanai Dake Jihar Filato Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe Tsaro
  • Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
  • Gaza Ga Albarusai Ga Yunwa Tsaro
  • Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
  • Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.