Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe
Published: February 1, 2026 at 5:10 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Wakilai ta yi Allah-wadai da munanan hare-haren ’yan bindiga a Gombe, ta nemi a ɗauki matakin soji cikin gaggawa.

Majalisar Wakilai ta amince da wani kudiri na gaggawa da ya shafi bukatun jama’a dangane da yawaitar hare-haren ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Akko ta jihar Gombe, waɗanda suka yi sanadin mutuwar akalla mutane shida, sace wasu 20, tare da lalata dukiyoyi na miliyoyin naira.

Kudirin, wanda Usman Bello Kumo ya gabatar, ya jawo hankalin ’yan majalisar kan sabbin hare-hare da aka kai cikin tsari a Garin Galadima, Pindiga, Garin Jaji, Laro da sauran al’ummomin da ke kewaye, lamarin da ya haddasa fargaba mai tsanani, kauracewar mazauna yankunan daga gidajensu, da kuma asarar hanyoyin samun abin dogaro.

Yayin gabatar da kudirin a zaman majalisa a Abuja, Kumo ya bayyana cewa hare-haren sun tilasta wa mazauna yankunan da dama gudun hijira, lamarin da ya ƙara tsananta matsalolin jin ƙai da kuma tabarbarewar tsaro a yankunan da abin ya shafa.

Bayan amincewa da kudirin, Majalisar ta yanke shawarar kira ga Hukumar Kula da bayar da agajin gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da Hukumar Raya Arewa maso Gabas (NEDC) da su gaggauta samar da kayan agaji ga waɗanda abin ya shafa da kuma mutanen da suka rasa muhallan su a al’ummomin da abin ya shafa.

Haka kuma, ’yan majalisar sun yi kira ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya gaggauta umartar Babban Hafsan Tsaro da ya ƙaddamar da haɗaɗɗiyar rundunar tsaro domin korar ’yan bindigar da rushe sansanoninsu, tare da hana faruwar irin waɗannan hare-hare nan gaba.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Yanbindiga sun Kashe mutun guda tare da yin garkuwa da mutane kimanin 100 a Jihar Nejan Najeriya.
Next Post: Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare Tsaro
Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
  • Afirka Ta Kudu Zata Fuskanci Koma Baya A Bangaren Samar Da Ayyukanyi Afrika
  • Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
  • Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani Labarai
  • Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.