Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe
Published: February 1, 2026 at 5:10 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Wakilai ta yi Allah-wadai da munanan hare-haren ’yan bindiga a Gombe, ta nemi a ɗauki matakin soji cikin gaggawa.

Majalisar Wakilai ta amince da wani kudiri na gaggawa da ya shafi bukatun jama’a dangane da yawaitar hare-haren ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Akko ta jihar Gombe, waɗanda suka yi sanadin mutuwar akalla mutane shida, sace wasu 20, tare da lalata dukiyoyi na miliyoyin naira.

Kudirin, wanda Usman Bello Kumo ya gabatar, ya jawo hankalin ’yan majalisar kan sabbin hare-hare da aka kai cikin tsari a Garin Galadima, Pindiga, Garin Jaji, Laro da sauran al’ummomin da ke kewaye, lamarin da ya haddasa fargaba mai tsanani, kauracewar mazauna yankunan daga gidajensu, da kuma asarar hanyoyin samun abin dogaro.

Yayin gabatar da kudirin a zaman majalisa a Abuja, Kumo ya bayyana cewa hare-haren sun tilasta wa mazauna yankunan da dama gudun hijira, lamarin da ya ƙara tsananta matsalolin jin ƙai da kuma tabarbarewar tsaro a yankunan da abin ya shafa.

Bayan amincewa da kudirin, Majalisar ta yanke shawarar kira ga Hukumar Kula da bayar da agajin gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da Hukumar Raya Arewa maso Gabas (NEDC) da su gaggauta samar da kayan agaji ga waɗanda abin ya shafa da kuma mutanen da suka rasa muhallan su a al’ummomin da abin ya shafa.

Haka kuma, ’yan majalisar sun yi kira ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya gaggauta umartar Babban Hafsan Tsaro da ya ƙaddamar da haɗaɗɗiyar rundunar tsaro domin korar ’yan bindigar da rushe sansanoninsu, tare da hana faruwar irin waɗannan hare-hare nan gaba.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Yanbindiga sun Kashe mutun guda tare da yin garkuwa da mutane kimanin 100 a Jihar Nejan Najeriya.
Next Post: Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
Rasha Takai Sabbin Hare-Hare Akan Wasu Biranen Ukraine Tsaro
Zamu Hada Kai Mu Yaki Cutar Shan’inna (Polio) Labarai
Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa Labarai
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
  • Muhawara Mai Zafi Tsakanin APC da ADC Shirye-Shirye
  • Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
  • Da Alamu Ronaldo Zai Buga Dukkan Wasanni Da Gasar Kofin Duniya A 2026 Wasanni
  • Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
  • Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025: Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.