Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Wakilan Majalisar Dokokin Phillipines Suna Yunkurin Tsige Shugaban Kasar
Published: February 3, 2026 at 10:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar talata, wakilan majalisar dokokin Phillipines suka yi zama domin yanke shawarar ko su ci gaba da sauraron karar neman tsige shugaban kasar Ferdinad Marcos Jr., wanda ake zargi da cin amanar kasa, rashawa, da kuma keta tsarin mulkin kasar.

Shugaba Marcos wanda yake tsakiyar wa’adin mulkinsa na shekaru shida, wanda ya musanta zargin, yana Fuskantar tuhuma da wani lauya dan gwagarmaya ya shigar gaban majalisar.

Idan har majalisa ta amince da zargin da ake yi wa shugaba Marcos, zai kasance shugaban kasar Phillipines na biyu da za’a tsige, na farko shine shugaba Joseph Estrada, wanda shari’arsa a shekara ta 2001 ta wargaje lokacin da wasu masu gabatar da kara suka fice daga inda ake shari’ar.

Laifuffukan da lauyan yake zargin shugaban na Phillipines sun hada da laifin sa a kama tsohon shugaban kasar Rodrigo Dutarte da mika shi ga kotun kasa da kasa mai hukunta manyan laifuffuka kan zargin da kotun take yi wa Dutarte na kashe duban mutane lokacin mulkinsa karkashin shirin yaki da miyagun kwayoyi.

Haka nan Marcos yana Fuskantar zarginsa kan yadda aka kashe dukiyar al’umma da ya kai ga abun fallasa kan ayyukan kare jama’a daga bala’in ambaliyar ruwa, da kuma zargin da ake yiwa shugaban kasar na mafani da miyagun kwayoyi, wadda idan ya tabbata ba zai cancanci ci gaba da shugabancin kasar ba.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar
Next Post: Kotun Daukaka Kara A Faransa Zata Tabbatar Da Hukuncin ‘Yan Jam’iyyar Ra’ayin Rikau

Karin Labarai Masu Alaka

Gabannin Harin Amurka Da Isra’ila Iran Farisa Ta Shirya Nata Afrika
Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
Bayan Shekaru Biyar, Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Gano Motar da Aka Sace A Fatakwal Afrika
Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • Kasar Jamus Ta Haramtawa Yara Kasa Da Shekaru 14 Hawa Dandalin Sada Zumunta Labarai
  • Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
  • China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
  • Magoya Bayan Obi Sun Yi Tutsu Gabanin Zaben 2027 Siyasa
  • Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
  • Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.