Babban sakataten MDD, Antonio Guterres, ya bayyana kawo karshen yin aiki da Yarjejeniyar Takaita Makaman Nukiliya a tsakanin Amurka da Rasha a zaman wani mawuyacin lokaci mai hatsari ga duniya, yana mai kira ga kasashen biyu da su gaggauta kulla wata sabuwar yarjejeniyar da zata maye gurbinta.
Yarjejeniyar, wadda aka fi sani da lakabinta na NEW START, ta kare aiki dazun nan da misalin karfe 6 na safiyar Najeriya, kuma ta takaita adadin kundojin nukiliyar da Rasha da Amurka zasu iya girkawa, da kuma yawan makamai masu linzami na doron kasa ko wadanda ake jigilarsu a jiragen karkashin ruwa da zasu iya dana ma makaman nukiliya.
Guterres yace a karon farko cikin shekaru kusan 50, duniya tana fuskantar zama cikin yanayin da babu wani shirin da ya takaita irin makaman nukiliyar da Rasha da Amurka zasu iya girkawa. Yace wadannan kasashe biyu sune suka mallaki kusan dukkan makaman nukiliyar da ake da su a duniya.


