Ministan harkokin wajen kasar Iran, Abbas Araqchi ya ce tattaunawar da ake tsakanin kasar sa da Amurka a Oman, inda Oman din ta zama me sulhuntawa, ya fara da nasara, kuma yana sa ran za’a dore a haka, a wani furuci da yayi da zai taimaka wajen kawar da fargabar da ake yi na cewa rashin cimma yarjejeniya zai iya tsunduma gabas ta tsakiya barkewar yaki.
Sai dai kuma ministan yace bayan tattaunawar a Muscat, babban birnin kasar Oman, suna bukatar duk wata ganawa Ayi ta ba tare da barazana ko matsin lamba ba. Ya ce Tehran zatayi magana ne kawai kan makamanta na nukiliya, ba zata yi magana kan wani abu ba kuma da Amurka.
Yayin da duka bangarorin biyu suka amince da farfado da huldar diplomasiyya tsakanin su kan takaddamar da ke tsakanin Iran da kasashen yamma game da makaman ta na nukiliya, fadar Washington ta so ta fadada tattaunawar zuwa makamai masu linzami da Iran din ta mallaka. Su kuma hukumomin Iran sun ce baza su tattauna kan hakan ba.


