Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje
Published: February 7, 2026 at 10:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar kula da kasuwannin zuba jari ta Ghana, ta umarci kamfanonin saye da sayar da hannayen jari a kasar su rage zuba jari a kasashen waje, a kokarin da take yi na kare darajar kudin kasar da ake kira Cedi da samun daidito a harkokin tattalin arzikin kasar.

Ghana wacce babba ce a hako zinari da noman cocoa a duniya, yanzu take farfadowa daga matsanancin yanayi na tattalin arziki data juma bata fada irinsa ba, ana sa ran zata kammala zagaye na uku na mu’amalarta da asusun bada lamuni na duniya da ake kira IMF a takaice cikin watan Agustan bana.

A cikin wata sanarwa data bayar wajajen maraicen ranar jumma’a, hukumar tace nan take hukumar ta haramtawa masu kamfanonin zuba jari amfani da fiye da kashi 20 cikin dari na jarinsu a kasashen waje, yayinda masu zuba jari da ada aka basu damar zuba jari na kachokan kudade da suke hanunsu, yanzu za’a kayyade suyi amfani da kashi 70 cikin dari na kudade da suke dashi.

Hukumar tace, tilas kamfanonin saye da sayar da hannayen jari su zuba jari a kasashen da hukumomi irinta suke musayar bayanai da ita hukumar ta Ghana.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara
Next Post: Muhawara Mai Zafi Tsakanin APC da ADC

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
Fiye Da Mutane 200 Sun Rasa Rayukansu A Wajen Hakar Ma’adanai Labarai
Ansamu Girgizar Kasa A Kasar Taiwan Labarai
Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea Labarai
  • Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da Shugaba Tinubu Siyasa
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.