Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje
Published: February 7, 2026 at 10:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar kula da kasuwannin zuba jari ta Ghana, ta umarci kamfanonin saye da sayar da hannayen jari a kasar su rage zuba jari a kasashen waje, a kokarin da take yi na kare darajar kudin kasar da ake kira Cedi da samun daidito a harkokin tattalin arzikin kasar.

Ghana wacce babba ce a hako zinari da noman cocoa a duniya, yanzu take farfadowa daga matsanancin yanayi na tattalin arziki data juma bata fada irinsa ba, ana sa ran zata kammala zagaye na uku na mu’amalarta da asusun bada lamuni na duniya da ake kira IMF a takaice cikin watan Agustan bana.

A cikin wata sanarwa data bayar wajajen maraicen ranar jumma’a, hukumar tace nan take hukumar ta haramtawa masu kamfanonin zuba jari amfani da fiye da kashi 20 cikin dari na jarinsu a kasashen waje, yayinda masu zuba jari da ada aka basu damar zuba jari na kachokan kudade da suke hanunsu, yanzu za’a kayyade suyi amfani da kashi 70 cikin dari na kudade da suke dashi.

Hukumar tace, tilas kamfanonin saye da sayar da hannayen jari su zuba jari a kasashen da hukumomi irinta suke musayar bayanai da ita hukumar ta Ghana.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara
Next Post: Muhawara Mai Zafi Tsakanin APC da ADC

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa Afrika
Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya Labarai
Tsarin Haraji Mai Cike Da Ayoyin Tambaya Na Shirin Fara Aiki Labarai
Iran Da Amurka Sun Gindayawa Juna Ka’idojin Tsagaita Wuta Afrika
Amurka Da Iran Sun Cimma Yarjejeniya Tsagaita Wuta Na Makonni Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
  • Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
  • Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
  • Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.