Matsalar rashin tsaro na ci gaba da zama karfen kafa a Najeriya duk kuwa da kokarin da hukumomin kasar ke cewa sunayi wajan shawo kan matsalar,
Akan haka ne Masarautar Borgu da Kuma shugaban makarantar St Mary ta Garin papiri suka gudanar da wani taron manema domin kara nunawa duniya halin tashin hankali da yankin Ke cikin,
Alh Murtala Halliru Dantoro shine yayi Magana a madadin Masarautar Borgu yace suna Bukatar Gwamnatin Bola Ahmed Tinumbu ta waiwaye yankin na Borgu..
Anashi gefen shugaban makarantar St Mary ta garin papiri wanda dama shine shugaban kungiyar kiristoci ta CAN a Jihar Neja Rev.Bu
lus Yuhanna yace mutanen da ake yima mummunan kisa a yankin sun hada da Musulmi da kiristoci saboda haka lamarin Yana da matukar tayar da hankali.
Shugaban karamar Hukumar Kayama hon.Abubakar Danladi shine shugaban karamar Hukumar Kayama a Jihar kwara Mai iyaka da Masarautar ta Borgu bayan harin nan woro da aka Hallaka Mutane 170 yace bukatarsu samar da sassanin Sojoji a Dajin Kainji Domin kawar da Mayakan Kungiyar jihadi ta ISWAP da suka mamaye Daji.
Ayanzu bayanai sun tabbatar da cewa hatta namun daji da akasan gandun dajin na Kainji dashi sun kaura sun bar maharan na cin karensu babu babbaka a dajin.

