Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro
Published: February 20, 2026 at 12:19 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu da takwaran aikinsa na Jamus Chancellor Friedrich Merz, sun tattauna ta wayar tarho kan batun tsaro, makamashi lantarki, da kuma kayayyakin more rayuwa, kamar yadda ofishin shugaban kasan ya fada a ranar Alhamis.

A maganar da suka yi ranar Laraba, na tsawon minti tara, shugabannin biyu sunyi magana kan sake farfado da aikin samar da wutan lanatarki a Najeriya da ya tsaya, da babban kamfanin kasar Jamus SIEMENS zai yi, haka kuma Najeriya zata sayi jirage masu saukar ungulu wadanda ba sababbi bane daga Jamus.

Shugaba Tinubu ya gayawa Mr. Mertz cewa Najeriya tana bukatar taimako wajen sabunta hanyoyin samarda wutan lantarki a kasar.

Wata yarjejeniyar da Najeriya ta kulla da kamfanin SIEMENS a shekara ta 2019, kamfanin zai sabunta hanyoyin raba wutan lantarki da bankunan Jamus za su dauki nauyin aikin, da zimmar idan aka kamala aikin zai samar da wutan lantarki MegaWatts dubu 7, zuwa 2021, sannan ya karu zuwa megawatt dubu 11 zuwa karshen Shekara ta 2023, sai dai aikin ya fuskanci kalubale daban daban da suka hada da kudi, sharuddan gwamnati da makamantar su.

Shugaba Merz na Jamus ya fadawa shugaba Tinubu cewa kamfanin SIEMENS zai yi aikin, kuma a shirye Bankin Deutsche yake ya samar da kudaden tafiyar da aikin, kamar yadda sanarwa daga ofishin shugaban kasar ya fada.

Najeriya da Jamus suna da huldar difilomasiyya na tsawon shekaru 65.

Labarai, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato
Next Post: Lakurawa Sun Kashe A Ƙalla A Mutane 34 A Jihar Kebbi

Karin Labarai Masu Alaka

Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Sojin Saman Najeriya Sun Lalata Sansanonin ‘Yan Ta’adda Afrika
Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa
  • Dan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APM A Bauchi Ya Bada Gudummawar Naira Miliyan ₦21 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bara Da Shira

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Hare Hare A Kasar Congo Ya Jikkata Mutane Da Dama Afrika
  • An Shirya Taron Horas Da Matasa Gabanin Wasan Motsa Jiki 2025 Wasanni
  • Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
  • Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai
  • “Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
  • Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.