A Benin ’yan bindiga sun kashe sojoji 15 suka jikkata wasu biyar a wani sansanin soja dake arewacin kasar,kamar yadda wani Kakakin sojan kasar ya fada ranar Juma’a, yayinda tarzoma take kara bazuwa a kasashe da suke yammacin Afirka.
‘Yan Bindiga masu alaka da al-Qeada da ISIS suna ci gaba da kai hare hare akan iyakoki da dazukan da suke tsakanin jamhuriyar Nijar, da Benin da kuma Najeriya, sun mai da yankin a zaman fagen daga.
Wata kungiya mai alaka da al-Qeada da ake kira Jama’at Nusrat al-Islam wal-muslim ta dauki alhakin kai wannan hari a Benin, kunigyar tace ta kai harin ne a wani wuri da ake kira Kofouno dake arewacin Benin, a ranar Laraba.
Kakakin sojojin Benin kanal James Johnson, yace sojojin sun kashe akalla hudu daga cikin mayakan lokacin da suke gudu kan baburansu. Ya karyata ikirin da ‘yan binidgar suka yi cewa sansanin sojojin yana hanunsu.
Benin, bata cika magana kan tarzomar da ‘yan bindiga suke haddasawa a arewacin kasar ba, kodashike cikin watan Afrilun bara ta ce wannan kungiya ta ‘yan bindiga mai lakabin JNIM a takaice a wani hari da ta kai ta kashe sojoji kasar 54.


