Majalisar kwararru a kasar Iran ta ayyana Mojtaba Khameini a matsayin sabon shugaban addini, domin maye gurbin mahaifinsa, marigayi Ayatollah Ali Khameini, yayin da Iran take kara nuna jajircewa da hare-haren da ake kai mata, kuma a yayin da yawan sojojin Amurka da suka mutu ya karu zuwa 7.
Mojtaba Khameini wanda ke tsaka-tsaki cikin jerin manyan malamai na Iran, yana da alaka mai karfi da rundunar sojojin juyin juya hali na Iran, har aka yi ta ganinsa a matsayin wanda zai iya gadon mahaifinsa.
Duk da cewa akidar Shi’a ta Iran ba ta karfafa gadon mulki daga uba zuwa da, Mojtaba ya kasance yana da magoya baya masu yawa da karfi a rundunar ta juyin juya hali da kuma ofishin shugabancin addini na mahaifinsa.
Isra’ila ta yi barazanar kai farmaki a kan duk wanda za a zaba, yayin da shi ma shugaba Donald Trump na Amurka ya bukaci da ya taka rawa wajen zaben sabon shugaban.
A ranar lahadi, Amurka ta ba da sanarwar mutuwar sojanta na 7 daga raunukan da ya samu a hare-haren ramuwar gayya na farklo da kasar Iran ta kai a makon da ya shige.
Wannan na zuwa kwana guda a bayan da Trump ya jagoranci bukin tarbar gawarwakin sojoji 6 da aka kashe tun fari.
A yayin da Trump yake fadin cewa tilas Iran ta mika wuya, kakakin majalisar dokokin Iran, Mohammed Bagher Qalibaf, yace ba su neman a tsagaita wuta a wannan yakin, kuma zasu lallasa wadanda suka kai musu farmaki.


