Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran
Published: March 11, 2026 at 4:19 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka da Isra’ila sunyi luguden wuta kan Iran a jiya talata, da ma’aikatar tsaron Amurka da ake kira Pentagon da Farisawan suka ce shine hari mafi tsanani tun fara yakin, duk da tsammanin da kasuwannin sayar da hannayen jari na duniya suka yi cewa shugaba Donald Trump zai kawo karshen yakin bada jumawa ba.

Kara jawo kalubale ga tattalin arzikin duniya, rundunar juyin juya hali ta Iran tace zata hana jigilar mai daga yankin Gulf idan Amurka da Isra’ial basu tsaida kai mata hari ba.

Sakataren ma’aikatar Tsaron Amurka Pete Hegseth yace “yau zata kasance rana da muka fi tsananta kai hare hare a cikin Iran, jiragen yaki mafi yawa, tare da amfani da bayanan sirri mai inganci,” inji sakataren a wani taro da manema labarai.

Mazauna birnin Tehran da suka yi magana da kamfanin dilancin labarai na Reuters bisa sharadin ba za’a bayyana sunayen su ba, suka ce babu inda jiragen yakin suka bari a birnin Tehran. Tace sai ka dauka jahannama. Tace ‘yayanta har tsoron bacci suke yi.

Duk da haka, kalaman shugaba Trump ranar Litinin cewa, “kusan an kammala yakin,” masu zuba jari sunyi amannar yakin zai kare nan ba da jumawa ba, kamin kassarawar da aka yi wa jigilar makamashi ta durkusar da tattalin arzikin duniya.

Shugabannin Iran suna ci gaba da nuna turjiya ko a yau talata. “Hakika bama neman a tsagaita wuta, mun hakikance cewa tilas a kwabi bakin mai tsaukana, saboda su koyi darasi, har abada ba za su kaiwa Iran hari ba, inji a kakakin majaisar dokokin kasar, Mohammmed Baqer Qalibaf, a shafinsa na X.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran
Next Post: Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta Afrika
Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika
Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amy Hunt Ta Zama Sabuwar Tauraruwar Wasannin Guje-guje Ta Birtaniya Wasanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari A Lebanon Afrika
  • Ɗan Jaridar Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Najeriya Kan Rashin Ingantattun Filayen Wasanni Wasanni
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya Afrika
  • Zamu Tarwatsa Cibiyoyin Makamashi Da Cibiyoyin Mai Din Iran Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.