Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa tace ta saukaka wa al’umma hanyoyin yin rajistan katin zabe ta hanya binsu har inda suke don yi musu rajista, gabanin babban zabe mai zuwa a shekarar badi.
Kwamishinan hukumar zabe ta kasa a jihar Filato, Muhammad Abubakar Sadiq yace matasa na da damar yin rajistan cikin sauki.
Sakataren ECWA, Rabaran Ayuba Asheshe ya yi huduba ne kan hadin kai don samun zaman lafiya.
A bangare guda kuwa, Alhaji Lawal Baba-Otu, jakadan yaki da shaye-shaye a Najeriya ya ja hankalin al’umma ne kan yin rajistan katin zaben da mai da hankali wajen zaben wadanda zasu cire musu kitse a wuta.
Hukumar zaben ta kuma yi kira wa dubban mutane da basu karbi katin zaben da suka yi a shekarun baya ba, su garzaya ofisoshin Hukumar dake kananan hukumomi, don samun damar gudanar da zabe a shekara ta dubu biyu da ishirin da bakwai.
Daga Jos Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton


