Ranar talata, Isra’ila ta bada sanarwar ta kashe babban jami’in tsaro a Iran, jami’in Farisa mafi-girma da ta auna hari akansa tun fara bayanin ranar farko na fara yakin, a yayinda wani jami’in kasar yake cewa, sabon shugaban addinin kasar ya ki amincewa da tayin sassauta rikicin, da wata kasa mai shiga tsakani ta gabatar mata.
Nan take dai Iran bata ce komi ba kan sanarwar da Isra’ila ta bayar cewa ta kashe Ali Larijani, wanda ake kallo a zaman mai fada aji kuma na hanun daman marigayi tsohon shugaban addinin kasar, da magajinsa kuma dansa Mojtaba.
A wata alamar ci gaba da bijirewar da Iran take yi, bayan fiye da mako biyu ana gwabza yaki, wani babban jami’in kasar, wanda ya bukaci a sakaye sunansa, yace Mojtaba Khameni yayi watsi da wani daftari da aka gabatarwa ma’aikatar harkokin wajen kasar na bukatar, “ a sassauta rikicin, ko a tsagaita wuta tsakaninta da Amurka,” Inji jami’in.
Jami’in yace sabon shugaban addinin kasar yayi zaman farko na shawarwari game da harkokin wajen kasar, sai dai bai fayyace ko sabon shugaban wanda zuwa yanzu ba’a ganshi ba tunda aka nada shi, ya halarci zaman shawarwarin na farko da kansa, kodai ya halarci taron ne daga nesa tare da amfani da hanyoyin sadarwa na zamani.


