Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Sakataren Tsaron Amurka Yace Yaki Tsakanin Amurka Da Iran Zai Dauki Sabon Salon
Published: March 31, 2026 at 8:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya fada ranar talata cewa, kwanaki masu zuwa za su kasance masu gauni a yakin da Amurka take yi da Iran, ya kuma gargadi Tehran cewa, yakin zai kazance idan bata yarda aka cimma yarjejeniya ba kawo karshen yakin ko tsagaita wuta ba.

Rundunar juyin juya hali ta Iran, ta maida martani inda tayi barazanar auna hare haren kan kamfanonin Amurka da suke yankin daga ranar Laraba, rundunar tace kamfanoni da zata auna sun hada da Microsoft, da Google, da Apple, da Intel, da IBM, da Tesla, da kuma Boeing.

Tunda farko, Iran ta cinna wuta kan wani jirgin ruwa shake da mai, ba nesa da gabar Dubai, harin da Farisar ta kai na baya bayan nan kan jiragen kasuwanci a yankin na Gulf ko a mashigin ruwan Hormuz, tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da hare hare kan kasar ranar 28 ga watan Febwairu.

Jiya Litinin, shugaban Amurka Donald Trump yayi barazanar zai yi kaca-kaca da da cibiyoyin samarda makamashi na Iran, idan bata amince da yarjejenyar zaman lafiya, kuma ta bude mashigin ruwa na Hormuz ba, hanya ta cikin ruwa mai tasiri ga jigilar makamashi da duniya take amfani da shi wadda Iran ta rufe shi.

A yau talatan shugaba Trump ya soki kasashe da basu taimaka a yakin ba, da suka hada da Faransa da kuma Ingila, yace su gwada bajinta ko kawarin guiwa da suka rasa a baya, su kwato mashigin ruwa na Hormuz, su samowa kan su mai. Faransa da Italiya sun nuna rashin amincewar su da wasu matakan sojin da Amurka da Isra’ila suka dauka, kamar yadda wasu majiyoyi suka fada,wadda yake nuna rarrabuwar kawuna tsakanin kasashe dake cikin kungiyar tsaro ta NATO.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna
Next Post: Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika
Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
Hukumar Hakar Ma’adanai A Kasar Zambiya Ta Dakatar Da Ayyukanta Kimiya
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
  • Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
  • Farashin Danyen Mai Ya Farfado Fiye Da Kashi Daya Sauran Duniya
  • An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
  • Kasashen Amurka Da China Sun Matsawa Ghana Domin Rage Kudaden Haraji Afrika
  • Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
  • Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika
  • Kenya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kasar Rasha Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.