Sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya fada ranar talata cewa, kwanaki masu zuwa za su kasance masu gauni a yakin da Amurka take yi da Iran, ya kuma gargadi Tehran cewa, yakin zai kazance idan bata yarda aka cimma yarjejeniya ba kawo karshen yakin ko tsagaita wuta ba.
Rundunar juyin juya hali ta Iran, ta maida martani inda tayi barazanar auna hare haren kan kamfanonin Amurka da suke yankin daga ranar Laraba, rundunar tace kamfanoni da zata auna sun hada da Microsoft, da Google, da Apple, da Intel, da IBM, da Tesla, da kuma Boeing.
Tunda farko, Iran ta cinna wuta kan wani jirgin ruwa shake da mai, ba nesa da gabar Dubai, harin da Farisar ta kai na baya bayan nan kan jiragen kasuwanci a yankin na Gulf ko a mashigin ruwan Hormuz, tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da hare hare kan kasar ranar 28 ga watan Febwairu.
Jiya Litinin, shugaban Amurka Donald Trump yayi barazanar zai yi kaca-kaca da da cibiyoyin samarda makamashi na Iran, idan bata amince da yarjejenyar zaman lafiya, kuma ta bude mashigin ruwa na Hormuz ba, hanya ta cikin ruwa mai tasiri ga jigilar makamashi da duniya take amfani da shi wadda Iran ta rufe shi.
A yau talatan shugaba Trump ya soki kasashe da basu taimaka a yakin ba, da suka hada da Faransa da kuma Ingila, yace su gwada bajinta ko kawarin guiwa da suka rasa a baya, su kwato mashigin ruwa na Hormuz, su samowa kan su mai. Faransa da Italiya sun nuna rashin amincewar su da wasu matakan sojin da Amurka da Isra’ila suka dauka, kamar yadda wasu majiyoyi suka fada,wadda yake nuna rarrabuwar kawuna tsakanin kasashe dake cikin kungiyar tsaro ta NATO.


