Gwamnatin Tarayyar Najeriya, ta hannun Hukumar Makamashi ta Kasa (ECN), ta kaddamar da aikin samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana (Solar) mai karfin megawatt biyu (2MW) a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote (ADUSTECH) da ke Wudil a Jihar Kano.

Wannan aiki, wanda kudinsa ya kai naira biliyan 3.8, yana karkashin shirin nan na ‘Renewed Hope Solarization’ na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Baya ga aikin samar da wutar, an kuma kaddamar da fitilun kan hanya guda 200 masu amfani da hasken rana a cikin harabar jami’ar.
Darakta Janar na hukumar, Dr. Mustapha Abdullahi, tare da Ministan Kirkira, Kimiyya da Fasaha, Kingsley Tochukwu-Udeh, ne suka kaddamar da fara aikin a ranar Juma’a.
Dr. Abdullahi ya bayyana cewa an ba kamfanin da zai gudanar da aikin wa’adin watanni uku kacal domin kammalawa. Ya ce an tsara wannan aiki ne domin kawo karshen matsalar tsadar wutar lantarki da jami’ar ke fuskanta, inda take biyan naira miliyan 22.4 a kowane wata.
“Wannan aiki na Wudil yana bin sahu ne bayan makamancinsa da muka kaddamar a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano a watan Satumban 2025, inda ake sanya tsarin megawatt hudu (4MW), da kuma aikin da muka kaddamar a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK) a makon jiya,” in ji Dr. Abdullahi.
Ya kara da cewa an ba kamfanin Safiatu Global Resources Limited kwangilar a kan kudi naira biliyan 3.8, kuma ba za a kara ko sisi a kan kudin ba, sannan dole ne su kammala a cikin lokaci.
Binciken da hukumar ta gudanar ya nuna cewa jami’ar tana da dalibai da ma’aikata sama da 24,000, kuma bukatar wutar da take da ita ta kai tsakanin megawatt 12.3 zuwa 16.4. Sai dai, wutar da take samu daga kamfanonin rarraba wuta ba ta taka kara ta karya ba, yayin da janaretocin da take amfani da su ba sa iya daukar nauyin bukatar jami’ar.
A nasa jawabin, Ministan Kirkira, Kimiyya da Fasaha, Kingsley Tochukwu-Udeh, ya ce wannan aiki mataki ne na raya kasa a karkashin manufofin gwamnatin Tinubu na bunkasa ilimi da kirkire-kirkire ta hanyar samar da ingantaccen makamashi.
Shi ma a nasa bangaren, Shugaban Jami’ar, Farfesa Musa Tukur-Yakasai, ya nuna jin dadinsa da wannan gagarumin tallafi, inda ya ce wannan mataki zai kara bunkasa harkar bincike da koyarwa a jami’ar.


