Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Ambasada Ismail Yusuf Abba, ya sake jaddada aniyar hukumar na zurfafa fadakarwa da horar da maniyyata ta fuskar addini domin tunkarar aikin hajjin shekarar 2026.
Shugaban ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, 22 ga watan Afrilun 2026, yayin taron kaddamar da Tawagar Malamai (Ulama Team) na aikin hajjin bana, wanda aka gudanar a dakin taro na gidan hajji da ke Abuja.
Taron ya samu halartar manyan malaman Musulunci guda 120 da aka zabo daga sassan kasar nan, wadanda suka hada da Farfesa Mansur Ibrahim Sokoto, Sheikh Bala Lau, Sheikh Abdulmuhyi Nasir (wanda ya wakilci Sheikh Sani Yahaya Jingir), Sheikh Abdulrahman Olanrewaju Ahmed, Sheikh Nasir Adam, Sheikh Muhammad Kabir Haruna Gombe, Sheikh Usman Usman Dahiru Bauchi, da Dr. Isa Akindele Solahuddeen, da dai sauran manyan malamai.
Babban makasudin taron shi ne tattauna yadda za a mayar da hankali wajen ilimantar da maniyyata da ba su horo na musamman.
Ambasada Abba ya dorawa malaman nauyin taimakawa hukumar wajen gudanar da darusan fadakarwa cikin harsuna daban-daban kafin tafiya da kuma lokacin gudanar da ayyukan hajji a kasa mai tsarki.
Ya jaddada cewa malaman su tabbatar sun koya wa maniyyata sahihan rukunai da sharuddan aikin hajji dalla-dalla, domin su sauke farali yadda ya kamata.
Haka zalika, ya bukaci malaman da su kasance a shirye wajen ba da amsoshi ga tambayoyin alhazai, musamman idan suka fuskanci kalubalen da ka iya shafar ingancin aikin hajjinsu.
Baya ga ilimantarwa, tawagar malaman za ta shirya addu’o’i na musamman a wurare masu tsarki, musamman a filin Arfa, domin rokar wa Najeriya da shugabanninta zaman lafiya, hadin kai, tsaro, da bunkasar tattalin arziki.
A nasa bangaren, Farfesa Bashir Umar ya bukaci malaman da su ja hankalin alhazai su yi addu’ar samun nasarar babban zaben shekarar 2027 da ke tafe, ganin cewa aikin hajjin na bana zai gudana ne a daidai lokacin da kasar ke shirin fuskantar zaben.
Daga karshe, malaman sun jaddada muhimmancin shirya zukatan maniyyata ta fuskar hakuri, ikhlasi, da kuma sadaukar da kai ga Allah, inda suka bayyana shirinsu na ganin ‘yan Najeriya sun samu gamsasshen aikin hajji karbabbe.


