Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika

NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai
Published: April 26, 2026 at 2:17 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Ambasada Ismail Yusuf Abba, ya sake jaddada aniyar hukumar na zurfafa fadakarwa da horar da maniyyata ta fuskar addini domin tunkarar aikin hajjin shekarar 2026.

​Shugaban ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, 22 ga watan Afrilun 2026, yayin taron kaddamar da Tawagar Malamai (Ulama Team) na aikin hajjin bana, wanda aka gudanar a dakin taro na gidan hajji da ke Abuja.

​Taron ya samu halartar manyan malaman Musulunci guda 120 da aka zabo daga sassan kasar nan, wadanda suka hada da Farfesa Mansur Ibrahim Sokoto, Sheikh Bala Lau, Sheikh Abdulmuhyi Nasir (wanda ya wakilci Sheikh Sani Yahaya Jingir), Sheikh Abdulrahman Olanrewaju Ahmed, Sheikh Nasir Adam, Sheikh Muhammad Kabir Haruna Gombe, Sheikh Usman Usman Dahiru Bauchi, da Dr. Isa Akindele Solahuddeen, da dai sauran manyan malamai.

​Babban makasudin taron shi ne tattauna yadda za a mayar da hankali wajen ilimantar da maniyyata da ba su horo na musamman.

Ambasada Abba ya dorawa malaman nauyin taimakawa hukumar wajen gudanar da darusan fadakarwa cikin harsuna daban-daban kafin tafiya da kuma lokacin gudanar da ayyukan hajji a kasa mai tsarki.

​Ya jaddada cewa malaman su tabbatar sun koya wa maniyyata sahihan rukunai da sharuddan aikin hajji dalla-dalla, domin su sauke farali yadda ya kamata.

Haka zalika, ya bukaci malaman da su kasance a shirye wajen ba da amsoshi ga tambayoyin alhazai, musamman idan suka fuskanci kalubalen da ka iya shafar ingancin aikin hajjinsu.

​Baya ga ilimantarwa, tawagar malaman za ta shirya addu’o’i na musamman a wurare masu tsarki, musamman a filin Arfa, domin rokar wa Najeriya da shugabanninta zaman lafiya, hadin kai, tsaro, da bunkasar tattalin arziki.

​A nasa bangaren, Farfesa Bashir Umar ya bukaci malaman da su ja hankalin alhazai su yi addu’ar samun nasarar babban zaben shekarar 2027 da ke tafe, ganin cewa aikin hajjin na bana zai gudana ne a daidai lokacin da kasar ke shirin fuskantar zaben.

​Daga karshe, malaman sun jaddada muhimmancin shirya zukatan maniyyata ta fuskar hakuri, ikhlasi, da kuma sadaukar da kai ga Allah, inda suka bayyana shirinsu na ganin ‘yan Najeriya sun samu gamsasshen aikin hajji karbabbe.

Afrika, Labarai, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Ga Fili Ga Doki Dambarwar APC Da ADC
Next Post: Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci

Karin Labarai Masu Alaka

Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika
Shugaban Kasar Tunisiya Ya Tsawaita Dokar Da Baci A Kasar Labarai
Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar Raya Birane Ta Rushe Gine-Ginen Da Suka Keta Dokokin Tsara Birane A Gombe
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dan Hamayya Ya Amince Da Faduwa A Zaben Kasar Benin Afrika
  • Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
  • Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
  • Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.