Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci
Published: April 27, 2026 at 10:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yayin da shirye-shiryen babban zaɓen shekarar 2027 ke ƙara ƙarfi a Jihar Gombe, ƙungiyoyin fararen hula sun yi kira ga jam’iyyun siyasa da su ƙara ba mata dama a harkokin siyasa.

Ƙungiyar Gombe Network of Civil Society Organizations, GONET, tare da Gombe Women Agenda, GWA, sun buƙaci jam’iyyun siyasa su nuna ƙuduri wajen haɗa mata ta hanyar aiwatar da tsarin fifikon mata (affirmative action) da kuma goyon bayan samar da kujeru na musamman ga mata.

A cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da Ibrahim Yusuf da Dakta Leah Iliya Jalo suka sanya wa hannu a madadin GONET, ƙungiyoyin sun bayyana damuwa kan yadda har yanzu mata ke ƙarƙashin wakilci a muƙaman jagoranci da yanke shawara a jihar, duk da irin gagarumar gudunmawar da suke bayarwa ga ci gaban al’umma da kuma kusan daidaiton yawan su da maza.

Sanarwar ta danganta wannan gibi ba da ƙarancin ƙwarewa ko sha’awar mata ba, sai dai ga tsauraran matsalolin tsari, al’adu da kuma na kuɗi da ke cikin tsarin siyasa da jam’iyyu, waɗanda ke hana mata shiga harkokin siyasa yadda ya kamata.

Ƙungiyoyin sun jaddada cewa tsarin fifikon mata da kujerun musamman bai kamata a ɗauke su a matsayin wata gata ba, sai dai a matsayin matakan gyara domin kawar da tsofaffin rashin adalci da kuma tabbatar da shugabanci mai haɗa kowa da kowa.

Sun kuma ce ingantacciyar dimokuraɗiyya dole ne ta wakilci bambancin jama’a, tare da gargadin cewa ware mata daga jagoranci na rage ingancin shugabanci da kuma tauye ci gaba.

Daga ƙarshe, sun buƙaci jam’iyyun siyasa da su ɗauki matakai na musamman, ciki har da aiwatar da dokokin fifiko ga mata, amincewa da kudirin kujerun musamman ga mata, ware kaso mai tsoka na tikitin takara ga mata, rage ko soke kuɗin fom ɗin takara, da kuma samar da tsare tsaren tallafi kamar horo da kariya daga tashin hankali na siyasa.

Sun kuma yi kira ga shugabannin jam’iyyu da masu ruwa da tsaki da su ɗauki mataki cikin gaggawa, suna mai cewa zaɓen 2027 wata muhimmiyar dama ce ta inganta daidaito tsakanin jinsi da kuma ƙarfafa dimokuraɗiyya a Jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan Labarai
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci
  • Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci
  • NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
  • Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
  • Farashin Danyen Mai Da Iskar Gas Ya Tashi Afrika
  • Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
  • Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.