Yayin da shirye-shiryen babban zaɓen shekarar 2027 ke ƙara ƙarfi a Jihar Gombe, ƙungiyoyin fararen hula sun yi kira ga jam’iyyun siyasa da su ƙara ba mata dama a harkokin siyasa.
Ƙungiyar Gombe Network of Civil Society Organizations, GONET, tare da Gombe Women Agenda, GWA, sun buƙaci jam’iyyun siyasa su nuna ƙuduri wajen haɗa mata ta hanyar aiwatar da tsarin fifikon mata (affirmative action) da kuma goyon bayan samar da kujeru na musamman ga mata.
A cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da Ibrahim Yusuf da Dakta Leah Iliya Jalo suka sanya wa hannu a madadin GONET, ƙungiyoyin sun bayyana damuwa kan yadda har yanzu mata ke ƙarƙashin wakilci a muƙaman jagoranci da yanke shawara a jihar, duk da irin gagarumar gudunmawar da suke bayarwa ga ci gaban al’umma da kuma kusan daidaiton yawan su da maza.
Sanarwar ta danganta wannan gibi ba da ƙarancin ƙwarewa ko sha’awar mata ba, sai dai ga tsauraran matsalolin tsari, al’adu da kuma na kuɗi da ke cikin tsarin siyasa da jam’iyyu, waɗanda ke hana mata shiga harkokin siyasa yadda ya kamata.
Ƙungiyoyin sun jaddada cewa tsarin fifikon mata da kujerun musamman bai kamata a ɗauke su a matsayin wata gata ba, sai dai a matsayin matakan gyara domin kawar da tsofaffin rashin adalci da kuma tabbatar da shugabanci mai haɗa kowa da kowa.
Sun kuma ce ingantacciyar dimokuraɗiyya dole ne ta wakilci bambancin jama’a, tare da gargadin cewa ware mata daga jagoranci na rage ingancin shugabanci da kuma tauye ci gaba.
Daga ƙarshe, sun buƙaci jam’iyyun siyasa da su ɗauki matakai na musamman, ciki har da aiwatar da dokokin fifiko ga mata, amincewa da kudirin kujerun musamman ga mata, ware kaso mai tsoka na tikitin takara ga mata, rage ko soke kuɗin fom ɗin takara, da kuma samar da tsare tsaren tallafi kamar horo da kariya daga tashin hankali na siyasa.
Sun kuma yi kira ga shugabannin jam’iyyu da masu ruwa da tsaki da su ɗauki mataki cikin gaggawa, suna mai cewa zaɓen 2027 wata muhimmiyar dama ce ta inganta daidaito tsakanin jinsi da kuma ƙarfafa dimokuraɗiyya a Jihar Gombe.


