Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya Afrika
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka

Hukumar NAHCON Fitar Da Jadawalin Fara Jigilar Alhazain Najeriya
Published: April 28, 2026 at 7:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar kula da aikin Hajji ta Najeriya (NAHCON), ta ce a ranar 3 ga watan Mayun shekarar 2026 ne za a fara jigilar maniyyata daga Najeriya zuwa Kasar Saudiyya, domin gudanar da ibadar aikin Hajjin bana.

NAHCON ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da Mataimakiyar Daraktan Yaɗa Labarai, Fatima Sanda Usara, ta fitar, inda ta ce jirgin farko na kamfanin FlyNas zai tashi daga sabon filin jirgin sama na Kasa-da-Kasa na Gateway da ke Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.

Baya ga jihar Ogun, sauran jiragen da za su tashi a wannan rana sun haɗa da Kamfanonin Umza da Max Air, da za su kwashe maniyyatan jihohin Kogi da Nasarawa daga Abuja, sai Kamfanin Air Peace da zai kwashe maniyyatan jihar Oyo daga Legas.

Kazalika daga Birnin Kebbi, wani jirgin na FlyNas zai tashi da maniyyatan Jihar Kebbi.

Tuni jami’an NAHCON da suka haɗar da tawagar likitoci suka sauka a ƙasar Saudi Arabiya a ranar Talata, 28 ga watan Afrilu, domin yin shirye-shiryen tarɓar maniyyatan Najeriya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa
Next Post: Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika
Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe
  • Hukumar NAHCON Fitar Da Jadawalin Fara Jigilar Alhazain Najeriya
  • Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya
  • UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sama da mutane dubu 500 ne yanbindiga suka kora daga gidajensu a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai
  • Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa Amurka
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
  • Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da Shugaba Tinubu Siyasa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.