Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika

Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato
Published: April 29, 2026 at 3:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A wani mataki na fitar da jihar Filato dake Najeriya daga kangin tashe-tashen hankula da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da shugabannin jihar, inda ya ba su umarnin komawa gida su fuskanci juna da zuciya ɗaya domin samar da dawwamamen zaman lafiya.

Haka zalika, Gwamnatin Tarayya ta amince da sakin kudi har Naira Biliyan biyu (N2bn) a matsayin tallafin gaggawa ga mutanen da harin ranar 29 ga watan Maris ya rutsa da su a unguwar Anguwan Rukuba da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa.

Yayin taron wanda aka kwashe sa’o’i uku ana tattaunawa a fadar Shugaban Kasa da ke Abuja ranar Talata, Shugaba Tinubu ya bayyana cewa lokaci ya yi da shugabanni a kowane mataki za su cire son zuciya, su rungumi juna domin kawo karshen asarar rayuka da dukiyoyi.

“Ba maganar biki muke yi a nan ba,” in ji Shugaban Kasan. “Muna nan ne domin mu faɗawa juna gaskiya. Idan ana amfani da matasa ana rura wutar gaba da kisan juna, ku shugabanni ya kamata ku fara bincikar kanku.”

Shugaban ya kuma kalubalanci tawagar, karkashin jagorancin Gwamna Caleb Mutfwang, da su koma su duba duk wasu rahotannin tsofaffin kwamitoci (White Papers) da aka taɓa yi kan rikicin jihar, su fito da hanyoyin da za a bi wajen aiwatar da su.

Tawagar mai mutum 32 ta haɗa da tsofaffin gwamnonin jihar; Sanata Simon Lalong, Sanata Jonah Jang, Joshua Dariye da Sir Fidelis Tapgun. Sauran sun hada da Sarkin Wase, Mai Martaba Mohammed Haruna; Gbong Gwon Jos, Da Jacob Gyang Buba; Shugaban kungiyar CAN na jihar, da kuma wakilan matasan Musulmi da Kirista.

A nashi ɓangaren, Gwamna Mutfwang ya nuna farin cikinsa, inda ya bayyana cewa wannan ne karon farko da dukkan tsofaffin gwamnonin jihar suka zauna a daki guda domin tattauna makomar jihar. Ya bayyana cewa wannan wata sabuwar baraka ce ta hadin kai da za ta taimaka wajen maido da martabar “Gidan Zaman Lafiya da Shakatawa.”

Shima Mai Martaba Gbong Gwon Jos, Da Jacob Gyang Buba, ya jinjinawa Shugaban Kasan, ya kuma bukaci a tura karin jami’an tsaro da kuma sanya na’urorin CCTV a lungu da sako na birnin Jos. Haka zalika, ya roki Shugaban da ya taimaka wajen ganin ’yan gudun hijira (IDPs) sun koma gidajen iyaye da kakanninsu kafin damuna ta kankama.

Taron ya zo ne a matsayin cika alkawarin da Shugaba Tinubu ya yi na zama da masu ruwa da tsaki na jihar bayan munanan kashe-kashen da aka yi a watan Maris, inda ya jaddada cewa ba za a zuba ido ana kisan mutane ba tare da an hukunta wadanda ke rura wutar rikicin ba.

Masana na ganin cewa wannan zama na Abuja zai iya zama silar kawo karshen shekaru da dama na gaba da jidali a jihar, muddin shugabannin suka yi amfani da wannan damar wajen girmama juna da adalci.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano
Next Post: Mohammed Abdullahi Abubakar Ya Sayi fom Don Tsayawa Takarar kujeran Gwamnan Bauchi A APC 2027

Karin Labarai Masu Alaka

Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika
Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
Kungiyoyi Sunyi Hasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka Afrika
Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kotun Amurka Ta Soke Harajin Fito Da Shugaba Trump Ya Kakabawa Kayan Kasashen Waje Amurka
  • Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.