Najeriya Da Maroko Za Su Kulla Yarjejeniya a fannin makamashi, noma, da kuma harkokin cinikayya
Alaƙar diplomasiyya tsakanin kasashen Najeriya da Maroko ta kara nuna ƙarfafa, inda kasashen biyu suka kulla yarjejeniyar karfafa dangantaka a fannonin makamashi, noma, da kuma harkokin cinikayya.
Wannan sanarwa ta fito ne bayan wata tattaunawa da aka yi tsakanin Ministar Harkokin Wajen Najeriya, Bianca Ojukwu, da takwaranta na kasar Maroko, Nasser Bourita.
Babban kashin bayan tattaunawar shi ne aikin ginin bututun iskar gas na Najeriya da Maroko (African Atlantic Gas Pipeline). Ministocin biyu sun bayyana wannan gagarumin aiki a matsayin “mai canza alkiblar tattalin arziki” wanda zai samar da tsaro a fannin makamashi da kuma dunkulewar yankin Afirka ta Yamma baki daya.
Ma’aikatar Harkokin Wajen ta tabbatar da cewa tuni kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) da takwaransa na kasar Maroko (ONHYM) suka kammala binciken fasaha na aikin. Ana sa ran Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Sarki Mohammed VI za su sanya hannu kan yarjejeniyar gudanar da aikin a rubuce kafin karshen rubu’i na hudu na wannan shekara.
Baya ga batun iskar gas, kasashen biyu sun tattauna hanyoyin hadin gwiwa wajen sarrafawa da rarraba takin zamani. Wannan mataki na da nufin tabbatar da wadatar abinci ba kawai a kasashen biyu ba, har ma da sauran sassan nahiyar Afirka.
Domin farfado da tsoffin yarjejeniyoyin da aka kulla tun zamanin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari a shekarar 2018, Najeriya na shirin karbar bakuncin taron hadin gwiwa na kasashen biyu (Bilateral Joint Commission) karo na biyu.
Haka zalika, ministocin sun jaddada bukatar sake kafa Majalisar Kasuwanci ta Najeriya da Maroko. Sun bayyana cewa yarjejeniyar cinikayya ta bai-daya ta nahiyar Afirka (AfCFTA) da kuma shirin kauce wa biyan haraji ninki biyu, za su bude sabbin kofofin bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu.


