An gudanar da bikin fitar da jadawalin wasannin Kofin Sarakunan jihar Gombe na shekarar 2026 cikin nasara a Cibiyar NITDA ICT da ke Jami’ar jihar Gombe, inda ya samu halartar sarakunan gargajiya, masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafa, ‘yan jarida da sauran baki daga sassa daban-daban na jihar Gombe

An shirya tare da daukar nauyin gasar ne daga GWG Sports. A yayin taron, an gabatar da sakonnin taya murna da fatan alheri daga masu ruwa da tsaki, sannan aka bayyana jadawalin wasannin kungiyoyin masarautu da na gargajiya da za su fafata a gasar.
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kwamitin Shirye-shiryen gasar Ahmad Shuaibu Gara Gombe, ya yaba wa sarakunan gargajiya da kafafen yada labarai bisa ci gaba da bayar da gudunmawa wajen bunkasa gasar. Ya ce masarautun jihar Gombe na da matukar rawar da suke takawa wajen samar da hazikan ‘yan wasan kwallon kafa da ke taimakawa ci gaban wasanni a jihar da ma kasa baki daya.
Ya kara da cewa an kirkiri wannan gasa ne domin karfafa hadin kai, inganta shigar matasa cikin harkar wasanni, da kuma gano sabbin basira a fadin jihar. Ya bayyana cewa an takaita shiga gasar ga kungiyoyin da aka yi rajista na masarautu da chiefdoms.
An gudanar da fitar da jadawalin karkashin jagorancin Shugaban Kwamitin Fasaha, Alhaji Abdulkadir Kawu, tare da Daraktan gasar, Haruna Isa Kalshingi, inda kungiyoyi suka zabi cibiyoyin wasannin su da suka hada da Kananan Hukumomin Funakaye, Deba da Billiri.
Haka kuma, taron ya samu halartar wakilan masarautu, jami’an kula da harkar kwallon kafa, da sauran masu ruwa da tsaki, wadanda suka yaba da cigaban gasar a matsayin wata hanya ta inganta zaman lafiya, hadin kai da bunkasa matasa ta hanyar wasanni.

An kammala taron ne da bayyana jadawalin wasanni a hukumance, addu’ar rufewa, da kuma daukar hoton tunawa tare da mahalarta daga masarautu da chiefdoms goma sha biyu na jihar Gombe


