Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

APC Ta Sauya Jerin ‘Yan Takararta Bayan Nazarin Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Fidda Gwani
Published: July 1, 2026 at 9:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC ta cire tsohon gwamnan jihar Benue, Gabriel Suswam, da wasu ‘yan takarar kujerar Sanata biyar daga cikin jerin sunayen ƙarshe da ta miƙa wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

Haka kuma, jam’iyyar ta cire tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Ondo, Gbenga Elegbeleye, tare da maye gurbin wasu ‘yan takarar majalisar wakilai guda 19 da suka yi nasara a zaɓen fidda gwani da aka gudanar a watan Mayun 2026.

A cikin wata wasiƙa da shugaban APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, da sakataren jam’iyyar na ƙasa, Ajibola Basiru, suka sanya wa hannu, jam’iyyar ta bayyana cewa sauye-sauyen sun biyo bayan rahoton Kwamitin Karɓar Ƙorafe-ƙorafe kan zaɓen fidda gwani.

Jihohin da sauye-sauyen suka shafa sun haɗa da Abia, Kogi, Taraba, Benue, Ebonyi, Ondo, Kaduna, Neja da Kwara.

Sai dai APC ta tabbatar da sunayen wasu fitattun ‘yan takara da za su fafata kujerun Sanata, ciki har da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Jibrin Barau, da gwamnoni AbdulRahman AbdulRazaq na Kwara, Hope Uzodimma na Imo, Ahmadu Fintiri na Adamawa da Muhammadu Inuwa Yahaya na Gombe.

Jam’iyyar ta ce ta karɓi sama da ƙorafe-ƙorafe 700 daga mambobinta dangane da zaɓen fidda gwani. Ta ƙara da cewa a halin yanzu fifikonta shi ne tabbatar da cewa duk ‘yan takarar sun cike takardun tsayawa takara tare da loda su a manhajar INEC kafin cikar wa’adin ranar 10 ga Yulin 2026.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas
Next Post: NITDA Da GOSIDEC Sun Horar Da Ma’aikatan Gombe Don Inganta Ayyukan Gwamnati

Karin Labarai Masu Alaka

An Harbo Jirgin Yakin Amurka A Iran Amurka
Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea Labarai
Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika
Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Talauci Ya Ragu A Tsakanin Al’ummar Jihar Jigawa Siyasa
  • Ukraine Da Syria Zasuyi Haɗin Gwiwar Tsaro Labarai
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika
  • Kasuwannin Hannayen Jari Suna Fuskantar Durkushewa Sakamakon Matsin Lambar Shugaba Trump Amurka
  • Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri Labarai
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
  • An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.