Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

CP Chuso Ya Yaba da Matakan Gwamnatin Gombe Wajen Rage Rikicin Makiyaya Da Manoma
Published: July 13, 2026 at 6:33 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya ce ci gaba da tattaunawa da kuma daukar matakin gaggawa kan matsalolin da ke tasowa shi ne mafita wajen hana rikice-rikicen makiyaya da manoma a jihar.

CP Chuso ya bayyana haka ne yayin taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki kan rikicin makiyaya da manoma da aka gudanar a Hedikwatar Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe.

Ya ce idan shugabannin al’umma a matakai daban-daban suka rika magance matsalolin tun kafin su rikide zuwa rikici, za a samu raguwar rikice-rikicen makiyaya da manoma.

Kwamishinan ‘yan sandan ya bayyana cewa dalilan rikicin makiyaya da manoma sun bambanta daga wannan yanki zuwa wani, don haka akwai bukatar duk masu ruwa da tsaki su hada kai wajen samar da mafita mai dorewa.


Ya yabawa Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa kafa kwamitocin sasanta rikice-rikice a matakai daban-daban, yana mai cewa hakan ya taimaka wajen rage nauyin da ke kan rundunar ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro.

Taron ya tattauna kan muhimman batutuwa da suka hada da mamaye hanyoyin shanun kiwo, samar da wuraren kiwo na zamani (ranches), zirga-zirgar dabbobi daga jiha zuwa jiha domin kiwo, da kuma hanyoyin gaggauta kai rahoton duk wata matsala domin daukar matakin da ya dace cikin lokaci.


Taron ya samu halartar sarakunan gargajiya, shugabannin addinai, shugabannin makiyaya na Fulani da suka Gudanar da jawabai amadadin mabiyansu Daga dukkan Sassan jihar Gombe da kuma manyan jami’an rundunar ‘yan sanda daga kananan hukumomi goma sha daya na jihar Gombe, domin karfafa hadin gwiwa wajen tabbatar da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugabannin Kiristocin Arewa Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Ummulkhairi
Next Post: An Bude Gasar Bauchi Annual International Polo 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa Afrika
Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC Afrika
Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado Amurka
‘Yan Sanda A Gombe Sun Jaddada Shirin Yaƙi Da Munanan Dabi’u Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo Labarai
  • Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
  • Shugaba Donald Trump Ya Nada Shugaban Bankin Tarayya Amurka
  • Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
  • ‘Yan Jaridar Gidan Gwamnatin Bauchi Sun Kammala Taron Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani Afrika
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.