Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
Published: August 7, 2026 at 6:40 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen jihar Gombe, ta amince da kafa Kwamitin Da’a da Ladabtarwa da kuma Kwamitin Jagoranci kan Hulɗa da ‘Yan Takarar Jam’iyyun Siyasa gabanin Babban Zaɓen shekarar 2027.

An cimma wannan matsaya ne a taron Majalisar Ƙungiyar (Congress) da aka gudanar a zauren taro na Ma’aikatar Yaɗa Labarai, Tsare-tsare da Al’adu ta Jihar Gombe, inda mambobi daga rassa daban-daban suka tattauna kan harkokin ƙungiyar da kuma makomar aikin jarida.

Kwamitin Da’a da Ladabtarwar, mai mambobi biyar, wanda Mista Peter Mele ke jagoranta, an kafa shi ne domin tabbatar da bin ƙa’idojin aikin jarida, kiyaye ɗa’a da ladabtar da duk wani memba da ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙungiyar.

Hakazalika, Majalisar ta kafa Kwamitin Jagoranci mai mambobi goma, ƙarƙashin shugabancin Chika Udenkwo, domin tsara tattaunawa tsakanin kafafen yaɗa labarai da ‘yan takarar jam’iyyun siyasa kafin zaɓen 2027.

An ce kwamitin zai shirya zaman tattaunawa da zai bai wa ‘yan takara damar gabatar da manufofinsu da tsare-tsaren ci gaba ga al’umma ta hanyar kafafen yaɗa labarai, domin bai wa masu zaɓe damar yanke hukunci bisa sahihan bayanai.

Majalisar ta kuma yi kira ga ‘yan siyasa, magoya bayansu da sauran masu ruwa da tsaki da su guji kalaman ƙiyayya, yaɗa labaran ƙarya, tunzura jama’a da duk wani nau’in tashin hankali da ka iya kawo cikas ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin Jihar Gombe.

Ta buƙaci jam’iyyun siyasa su mayar da hankali kan bayyana manufofinsu da shirye-shiryensu maimakon siyasar cin mutunci, yayin da shirye-shiryen Babban Zaɓen 2027 ke ƙara ƙamari.

Majalisar ta yabawa Gwamnatin Jihar Gombe bisa ayyukan ci gaba da take aiwatarwa, tabbatar da zaman lafiya da kuma goyon bayan da take bai wa aikin jarida.

Haka kuma, ta roƙi gwamnatin jihar da ta gaggauta kammala ginin Sakatariyar NUJ tare da miƙa shi ga ƙungiyar, tana mai cewa hakan zai ƙara inganta gudanar da ayyukanta.

Majalisar ta kuma buƙaci gwamnatin jihar ta taimaka wajen samar da sabuwar motar ƙungiyar domin maye gurbin wadda ta lalace a hatsarin mota da ya yi sanadin rasuwar wasu mambobinta.

Bugu da ƙari, Majalisar ta amince da kafa wani kwamiti da zai shirya Taron Zaman Lafiya, wanda zai haɗa jam’iyyun siyasa da ‘yan takara domin ƙarfafa siyasa cikin lumana, fahimtar juna da kuma tabbatar da dorewar dimokuraɗiyya a Jihar Gombe.

Da yake jawabi, Shugaban NUJ na Jihar Gombe, Kwamared Faruk Mu’azu, ya yabawa Kwamishinan Yaɗa Labarai, Tsare-tsare da Al’adu bisa samar da kyakkyawan wurin gudanar da taron da kuma ci gaba da tallafa wa walwala da bunƙasa aikin ‘yan jarida a jihar.

Majalisar ta kuma gode wa dukkan mambobinta bisa halartar taron, gudummawar da suka bayar da kuma jajircewarsu wajen bunƙasa haɗin kai da ci gaban ƙungiyar.

Sanarwar ta fito ne ɗauke da sa hannun Sakatare, Shuaibu Umar, a madadin Kwamitin Shirya Sanarwar Taron.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
Next Post: Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata

Karin Labarai Masu Alaka

Babban Bankin Najeriya Ya Rage Kudin Ruwa Da Kashi Daya Cikin Dari Labarai
Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda Afrika
An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC Afrika
Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci Afrika
  • Majalisar Dottawa Ta Kafa Komitin Dokar Zabe Najeriya
  • Kotun Amurka Tana Tuhumar Wani Dan Jarida Amurka
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
  • Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
  • An Tsaurara Tsaro Yayin Da Tehran Ke Shirin Karɓar Masu Jimamin Ayatollah Khamenei Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.