Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna Afrika
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi Afrika
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika

Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
Published: June 13, 2026 at 8:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An ƙaddamar da gasar Kofin Sarkin Gombe ta shekarar 2026 a ranar Asabar a filin wasan Pantami da ke jihar Gombe, tare da halartar sarakunan gargajiya, jami’an gwamnati, shugabannin wasanni da dubban masu sha’awar ƙwallon ƙafa.

Gasar, wadda ake gudanarwa duk shekara, tana haɗa masarautu da ƙananan hukumomin gargajiya daga sassan jihar domin ƙarfafa haɗin kai, zaman lafiya, fahimtar juna da kuma bai wa matasa damar nuna basirarsu ta fannin ƙwallon ƙafa.

Da yake jawabi a wajen bikin buɗe gasar, shugaban shirya gasar, Ahmed Shuaibu Gara Gombe, ya ce gasar ta zama wata muhimmiyar hanya ta gano da bunƙasa hazikan matasa a harkar wasanni tare da ƙarfafa zumunci tsakanin al’ummomin jihar.

Ya Bayyana cewa an bude Gasar da fafatawa Tsakanin Nafada da Gombe inda za’a Cigaba da bugawa a cibiyiyi uku da suka da da Cibiyar Bajoga, Deba da Billiri kuma Ya yabawa masarautu da suka yi rijista domin shiga gasar, yana mai bayyana cewa Masarautar Akko ce kaɗai ba ta shiga ba, tare da nuna fatan za ta shiga a bugu na gaba.

A nasa jawabin, Sarkin Gombe, Abubakar Shehu Abubakar III, wanda Madakin Gombe da Wakilin Birnin ya wakilta, ya jaddada goyon bayan masarautar ga gasar tare da yaba wa Ahmed Gara Gombe bisa ƙoƙarinsa na samar da damar bunƙasa matasa ta hanyar wasanni.

Shi ma shugaban Nigeria Football Federation, Ibrahim Musa Gusau, ya bayyana farin cikinsa kan yadda aka fara gasar, yana mai fatan za ta kasance mai cike da gasa cikin lumana da nuna bajinta.

Kamfanin GWG Sports Center Limited ne ya shirya tare da ɗaukar nauyin gasar ƙarƙashin jagorancin Ahmed Shuaibu Gara Gombe, a wani yunƙuri na ci gaba da tallafa wa ci gaban matasa da harkokin wasanni a jihar.

Masu bibiyar harkokin wasanni sun bayyana cewa Kofin Sarkin Gombe ya zama ɗaya daga cikin manyan gasa na matakin tushe a jihar, inda yake haɗa wasanni da al’adun gargajiya tare da ƙarfafa haɗin kan al’umma.

Ana sa ran wasannin za su ci gaba a makwanni masu zuwa yayin da ƙungiyoyi daga sassan Jihar Gombe ke fafatawa domin lashe kofin gasar ta shekarar 2026.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
Next Post: Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa

Karin Labarai Masu Alaka

MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan Afrika
Bahagon Mancha Ya Buge Bahagon Maitakwasara Da Wasun Su! Nishadi
Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya Najeriya
Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika
Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika
Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Fanny Amun Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Kwamitin Binciken NFF
  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi
  • Ceferin Ya Ce Ba Zai Yi Takarar Shugabancin FIFA Ba
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland Amurka
  • Duniyar Dambe A Makon Jiya Nishadi
  • Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai
  • Amurkawa Suna Turuwa Zuwa Kasar Faransa Duk Da Rashin Jituwa A Tsakanin Kasashen Amurka
  • Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
  • An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio Labarai
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.