Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe
Published: February 1, 2026 at 1:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 1, 2026

An Kaddamar da Kwamitin Gasar Kofin Haɗin Kan Masarautun Gargajiya na Gombe 2026

An kaddamar da Kwamitin Shirya Gasar Ƙwallon Ƙafa ta Haɗin Kan Masarautun Gargajiya na jihar Gombe dake arewa maso gabashin Najeriya, wadda aka fi sani da Kofin Haɗin Kan Sarkin Gombe 2026, a hukumance a birnin Gombe.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a taron farko na kwamitin, inda aka miƙa wa mambobinsa takardun shaidar aikinsu. Bayan haka, an gudanar da taron manema labarai da ya samu halartar wakilan manyan kafafen yaɗa labarai.

Da yake jawabi yayin taron, Shugaban Kwamitin kuma mai ɗaukar nauyin gasar, Ahmed Shuaibu Gara Gombe, ya bayyana cewa an shirya gasar ne domin ƙarfafa haɗin kai, zaman lafiya da kuma bunƙasa matasa ta hanyar wasanni a masarautun gargajiya na jihar.

Ya ƙara da cewa gasar za ta gudana ne da tsarin haɗaka, inda za a raba ƙungiyoyin da za su fafata gida huɗu a cibiyoyi huɗu, bisa shawarwarin da Kwamitin Fasaha zai bayar.

Ahmed Shuaibu Gara Gombe ya kuma sanar da kyaututtuka masu tsoka da aka tanada kuma kungiyar da ta zama zakara za ta samu naira miliyan biyar tare da kofi, ta biyu kuma naira miliyan uku, yayin da ta uku za ta samu naira miliyan biyu.

Haka kuma za a bayar da lambobin yabo na musamman ga Mafi Kyawun Mai Tsaron Raga, Wanda Ya Fi Zura Ƙwallaye, Fitaccen Ɗan Wasa na Gasar, da kuma Ƙungiyar da Ta Fi Nuna Wasan Gaskiya, duk tare da kofuna.

Mai ɗaukar nauyin gasar ya kuma bayyana cewa za a fara rangadin nuna kofin gasar a faɗin jihar daga Litinin, 2 ga Fabrairu, 2026, zuwa Jumma’a, 6 ga Fabrairu, 2026.

Rangadin zai zagaya dukkan masarautun gargajiya 15 na jihar, farawa daga Masarautun Nafada da Funakaye, sannan ya wuce Yamaltu, Deba, Waja, Kaltungo, Tangale, Akko, Pindiga, Cham, Dadiya, Tula, Gona, da Dukku.

Ana shirya gasar Kofin Sarkin Gombe ta 2026 ne tare da ɗaukar nauyinta daga kamfanin Green White Green Sports Center Limited, tare da goyon bayan Mai Martaba Sarkin Gombe.

Ana sa ran gasar za ta ƙara bunƙasa harkokin ƙwallon ƙafa a matakin tushe tare da ƙarfafa haɗin kai tsakanin al’ummomin jihar Gombe.

Kwamitin shirya gasar na ƙarƙashin jagorancin Ahmed Shuaibu Gara Gombe a matsayin Shugaba, yayin da Auwal Musa Umar, tsohon Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta jihar Gombe, ke matsayin Mataimakin Shugaba.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da masu riƙe da sarautun gargajiya da wakilan al’umma, yayin da Haruna Abdullahi yake a matsayin Sakatare da Yakubu Maikudi Jami’an yada labarai tare da masu kula da harkokin yaɗa labarai da tallafin tsare-tsare na Musamman.

Labarai, Najeriya, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga
Next Post: Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya. Wasanni
Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
Adamu: “Yakar Cin Hanci Daga Tushe Itace Mafita Daya Tilo” Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
  • Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar Afrika
  • Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco Afrika
  • Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
  • Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
  • Kocin Ranchers Bees Ya Yi Murabus Wasanni
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.