Matsalolin tsaro dake da fuskoki daban-daban da suka addabi al’ummar jihar Filato na dab da kawo karshe, bayan hukumomi sun fara gano wadanda ke warware kokarin zaman lafiya a jihar.
Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ne ya bayyana hakan, yayinda al’ummar musulmin jihar Filato suka kai masa gaisuwar Sallah a fadar gwamnatin jihar.

Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang wanda ya yaba da ziyarar na hada dankon zumunci a tsakanin gwamnati da al’umma, ya kuma ce sun fara fahimtar wadanda ke hana samun zaman lafiya kuma suna daukar matakai.
Alhaji Garba Abdulkadir, shine mataimakin shugaban kungiyar Jama’atu Nasril Islam a jihar Filato, yace manufar zuwansu shine don fatan Samun alkhairi.
Shima Alhaji Sani Mu’azu, Makaman Jos ta Arewa, yace al’ummar musulmi sun yi godiya ne saboda an gudanar da Sallah lafiya.
Mamba mai wakiltar shiyyar Jos ta Arewa maso Arewa, a majalisar dokokin jihar Filato, Adamu Aliyu yace suna bawa hukumomi shawarwari kan daukan matakan tsaro.
Al’ummar musulmin sun kuma mika wa gwamnan huhun goro, yayinda shima gwamnan na jihar Filato, Caleb Mutfwang ya mika musu nashi goron don nuna hadin kai da amincewa da juna,
Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos


