Kasar Chad ta fara sauyawa ‘yan gudun hijira dake sansanin iyakar ta da kasar Sudan matsuguni, yayin da take shirin aikewa da sojoji wajen don dakile hare-hare da ake kawo musu daga makwabtan nasu, kamar yadda wani jami’in kula da ‘yan gudun hijira na kasar ya shaidawa kamfanin dillancin labari na Reuters.
A makon da ya gabata, shugaban kasar Chadi Mahamat Idriss Deby ya umarci sojoji da su shirya daukan fansa bayan da wani hari na jirgi mara matuki na drone daga Sudan ya kashe musu mutane 17, ciki har da masu zaman makoki.
Za’a fara sauyawa ‘yan gudun hijira kimanin 2,300, wanda fiye da rabin su mata ne da yara, a cewar Saleh Tebir Souleymane, mai wakiltar hukumar kula da ‘yan gudun hijira na garin Tine, dake da iyaka da Sudan.


