Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika
  • Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika

Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya
Published: December 25, 2025 at 5:39 PM | By: Bala Hassan

Ba a maye gurbin Gbajabiamila da Muri-Okunola ba — Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya ta musanta wani labari na ƙarya da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sauya Shugaban Ma’aikatan Fadarsa (Chief of Staff), Hon. Femi Gbajabiamila, da Babban Sakataren Sirrinsa (Principal Private Secretary), Hakeem Muri-Okunola.

A cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar a ranar Alhamis, ta bayyana cewa babu wata gaskiya ko kaɗan a cikin wannan ikirari, tare da kira ga ’yan Najeriya da su yi watsi da labarin gaba ɗaya.

Sanarwar ta jaddada cewa Hon. Femi Gbajabiamila na nan daram a matsayin Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, yayin da Hakeem Muri-Okunola shi ma ke ci gaba da gudanar da aikinsa a matsayin Babban Sakataren Sirri. Ta ce babu wani sauyi da aka yi a wadannan mukamai.

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa labarin da ke yawo ƙirƙirarre ne daga wasu masu yaɗa labaran ƙarya da nufinsu shi ne tayar da zaune tsaye da rashin jituwa a cikin gwamnati.

Haka kuma, ta sake jan hankalin kafafen yaɗa labarai da masu amfani da kafafen sada zumunta da su rika tantance sahihancin duk wani bayani kafin wallafawa ko yadawa.

Sanarwar ta samu sa hannun Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, a ranar 25 ga Disamba, 2025.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu
Next Post: Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi

Karin Labarai Masu Alaka

An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi
  • Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya
  • Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai
  • Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane Labarai
  • Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
  • An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.