Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna Afrika
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi Afrika
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika

Gidauniyar Jalo Wali Ta Ƙaddamar Da Bada Audugar Mata A Gombe
Published: July 28, 2026 at 4:15 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Hukumar Raya Yankin Kudancin Gombe (Gombe South LCDA), Auwal Jauro Bapp, tare da mataimakinsa, Dalhatu Boderi, sun yaba da shirin rabon kayan tsaftar al’ada ga ‘yan mata da Alhaji Jalo Wali ya ƙaddamar. Sun bayyana shirin a matsayin wani muhimmin mataki da ya zo kan lokaci domin inganta lafiyar mata da kuma ƙarfafa ‘ya’yan mata su ci gaba da karatunsu ba tare da tangarda ba.

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban LCDA ya tabbatar wa masu shirya shirin da cikakken goyon baya da haɗin kai daga hukumarsa domin tabbatar da nasarar aiwatar da wannan shiri.

A nata jawabin, Shugabar Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Jauro Tudun Wada (GJSS), Zulaihat Kabir, tare da Auwalu Mai Matasa Pantami, Mahmud Abubakar Wamban Pantami da Hajiya Maimuna Saleh Abdu, sun yi tsokaci kan nasarorin da gwamnatin Gombe ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ta samu a fannoni daban-daban.

Sun kuma yi kira ga masu hannu da shuni da ƙungiyoyi masu zaman kansu su haɗa hannu da gwamnati wajen tallafa wa mata da yara a faɗin jihar.

Tun da farko, wanda ya assasa shirin, Alhaji Jalo Wali, ya bayyana cewa haɗin gwiwar da suka yi da Alhaji Sa’adu Ali Mai Silifas na da burin raba fakiti ɗari na kayan tsaftar al’ada ga ‘yan mata a makarantun firamare da ke dukkan ƙananan hukumomi goma sha ɗaya na jihar Gombe.

Ya ce manufar shirin ita ce wayar da kan ‘yan mata kan tsaftar al’ada tare da samar musu da kayan da za su taimaka musu su ci gaba da karatunsu cikin walwala.

Alhaji Jalo Wali ya kuma bayyana Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin ɗan takarar gwamna da ya cancanta, tare da yin kira ga al’ummar jihar Gombe su ci gaba da yi wa dukkan ‘yan takarar Jam’iyyar APC addu’ar samun nasara.

A nasa jawabin, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Gombe, Saleh Idris, da Sakataren Ilimi na ƙaramar hukumar wanda Abubakar Muhammad Bello (Bunun Gombe) ya wakilta, sun yaba wa Gombe Charity for Men and Women initiatives Foundation ƙarƙashin jagorancin Alhaji Jalo Wali da Alhaji Sa’adu Ali Mai Silifas bisa wannan shiri na jin ƙai.

Sun yi addu’ar Allah Ya saka musu da alheri tare da ƙara musu ƙarfin gwiwar ci gaba da gudanar da ayyukan tallafawa mata da ‘ya’yan mata a jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Rumbun Hotuna, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Next Post: Kwamitin Ardo Chindo Ya Buƙaci A Hana Mamaye Filayen Kiwo da Gandun Daji

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
AIG Kwaimo Ya Kai Ziyarar Aiki Gombe, Ya Buƙaci Ƙara Ƙaimi A Yaƙi Da Ta’addanci Labarai
Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba Sauran Duniya
Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama Najeriya
Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Fanny Amun Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Kwamitin Binciken NFF
  • Pasto Yohanna Buru Ya Jagoranci Kiristoci Wajen Bikin Mauludi Tare Da Musulmi A Kaduna
  • Tinubu Ya Buƙaci Musulmi Su Riƙe Haƙuri, Tawali’u Da Tausayi
  • Ceferin Ya Ce Ba Zai Yi Takarar Shugabancin FIFA Ba
  • Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
  • Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas Labarai
  • Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka Amurka
  • Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
  • Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula Labarai
  • Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika
  • Asusun IMF Zai Bawa Kasar Misra Lamunin Sama Da Dala Biliyan 2 Sauran Duniya
  • Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.