Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Gidauniyar Jalo Wali Ta Ƙaddamar Da Bada Audugar Mata A Gombe
Published: July 28, 2026 at 4:15 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Hukumar Raya Yankin Kudancin Gombe (Gombe South LCDA), Auwal Jauro Bapp, tare da mataimakinsa, Dalhatu Boderi, sun yaba da shirin rabon kayan tsaftar al’ada ga ‘yan mata da Alhaji Jalo Wali ya ƙaddamar. Sun bayyana shirin a matsayin wani muhimmin mataki da ya zo kan lokaci domin inganta lafiyar mata da kuma ƙarfafa ‘ya’yan mata su ci gaba da karatunsu ba tare da tangarda ba.

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban LCDA ya tabbatar wa masu shirya shirin da cikakken goyon baya da haɗin kai daga hukumarsa domin tabbatar da nasarar aiwatar da wannan shiri.

A nata jawabin, Shugabar Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Jauro Tudun Wada (GJSS), Zulaihat Kabir, tare da Auwalu Mai Matasa Pantami, Mahmud Abubakar Wamban Pantami da Hajiya Maimuna Saleh Abdu, sun yi tsokaci kan nasarorin da gwamnatin Gombe ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ta samu a fannoni daban-daban.

Sun kuma yi kira ga masu hannu da shuni da ƙungiyoyi masu zaman kansu su haɗa hannu da gwamnati wajen tallafa wa mata da yara a faɗin jihar.

Tun da farko, wanda ya assasa shirin, Alhaji Jalo Wali, ya bayyana cewa haɗin gwiwar da suka yi da Alhaji Sa’adu Ali Mai Silifas na da burin raba fakiti ɗari na kayan tsaftar al’ada ga ‘yan mata a makarantun firamare da ke dukkan ƙananan hukumomi goma sha ɗaya na jihar Gombe.

Ya ce manufar shirin ita ce wayar da kan ‘yan mata kan tsaftar al’ada tare da samar musu da kayan da za su taimaka musu su ci gaba da karatunsu cikin walwala.

Alhaji Jalo Wali ya kuma bayyana Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin ɗan takarar gwamna da ya cancanta, tare da yin kira ga al’ummar jihar Gombe su ci gaba da yi wa dukkan ‘yan takarar Jam’iyyar APC addu’ar samun nasara.

A nasa jawabin, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Gombe, Saleh Idris, da Sakataren Ilimi na ƙaramar hukumar wanda Abubakar Muhammad Bello (Bunun Gombe) ya wakilta, sun yaba wa Gombe Charity for Men and Women initiatives Foundation ƙarƙashin jagorancin Alhaji Jalo Wali da Alhaji Sa’adu Ali Mai Silifas bisa wannan shiri na jin ƙai.

Sun yi addu’ar Allah Ya saka musu da alheri tare da ƙara musu ƙarfin gwiwar ci gaba da gudanar da ayyukan tallafawa mata da ‘ya’yan mata a jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Rumbun Hotuna, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Next Post: Kwamitin Ardo Chindo Ya Buƙaci A Hana Mamaye Filayen Kiwo da Gandun Daji

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas Labarai
Iran Ta Bukaci Duniya Ta Shirya Domin Fuskantar Tsadan Mai Amurka
Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki Labarai
Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba” Wasanni
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari A Lebanon Afrika
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.