Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya yi Allah wadai da ƙaruwar hare-hare da kashe kashen da ake yi kwanan nan a sassan jihohin Kwara, Katsina da Benue, yana mai bayyana su a matsayin abin takaici, rashin hankali kuma cin zarafi kai tsaye ga al’ummar ƙasa baki ɗaya.
Wannan Allah wadai ya biyo bayan hare-haren da aka kai a ƙauyukan Woro da Nuku ne a Ƙaramar Hukumar Kaiama ta jihar Kwara, inda ake zargin ‘yan ta’adda sun kai hari a daren Talata da kisan aƙalla mutane 20 a ƙauyen Doma A da Doma B na Gundumar Tafoki, a Ƙaramar Hukumar Faskari ta jihar Katsina da kuma wani lamari na daban a ƙauyen Abande na gundumar Mbaikyor da Turan, a Ƙaramar Hukumar Kwande ta jihar Benue, inda aka ruwaito cewa an kashe mutane da dama.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a madadin Gwamnonin Arewa, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana matuƙar bakin ciki game da waɗánnan mummunan asarar rayuka na waɗanda ba su ji ba ba su gani ba, yana mai miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, da al’ummomin da abin ya shafa da kuma gwamnatoci da al’ummomin jihohin uku.
Gwamna Inuwa Yahaya ya yabawa Gwamnonin jihohin Kwara, Katsina da Benue bisa jagoranci da jajircewarsu a duk lokacin da ake fuskantar ƙalubalen tsaro da ake yawan fuskanta, yana mai bayyana ƙoƙarinsu na tallafawa al’ummomin da abin ya shafa, da ƙarfafa tsarin tsaro a yankin da kuma haɗa kai da hukumomin tarayya don farfaɗo da zaman lafiya.
Ya yi ƙira ga hukumomin tsaron ƙasar su ƙara himma wajen tattara bayanan sirri, da sanya ido da kuma ɗaukar matakan da suka dace na gano waɗanda suka aikata wannan laifi da kuma waɗanda ke tallafa musu, yana mai jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyi babban alhakin ne dake kan duk wani shugaba.
“Ƙungiyar Gwamnonin Arewa tana goyon bayan hukumomin tsaronmu kuma tana ƙira a garesu, su ɗauki duk wani matakin daya dace don gurfanar da masu laifin a gaban shari’a. Bai kamata masu aikata waɗannan laifukan su sha ba tare da hukunci ba,” in ji Gwamna Inuwa Yahaya.
Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin na Arewa ya tabbatarwa ‘yan Najeriya jajircewar Ƙungiyar ta yi na yin aiki tare da Gwamnatin Tarayya, da hukumomin tsaro, da masarautun gargajiya da shugabannin al’umma don magance matsalolin rashin tsaro ta hanyar haɗakar matakan tsaro masu ƙarfi, da tattara bayanan sirri da leƙen asiri da kuma samar da tallafi a harkokin tattalin arziƙi da zamantakewa na dogon lokaci.
Ya yi addu’ar Allah ya jiƙan waɗanda suka mutu, sannan ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki ya baiwa waɗanda suka ji rauni sauƙi, yayin da ya yi ƙira ga ‘yan ƙasar da su ci gaba da kasancewa cikin shiri tare da yin haɗin gwiwa da hukumomin tsaro don daƙile aika-aikar ta’addanci.


