Hukumar zartarwa ta Asusun bada lamuni na duniya, wato IMF ta amince da sake yin nazari a karo na 6, kuma na karshe akan kara wa’adin damar kasar Zambia na samun bashi, abinda zai share fagen bayar da dala miliyan 190.
Kasar da ke kudancin nahiyar Afirka, ta cimma yarjejeniyar samar da kudi dala miliyan dubu daya da dubu dari uku da IMF a shekarar 2022, don tallafawa tattalin arzikin ta, yayin da take neman mafita na kasa biyan bashi kan lokaci da ta yi, kafin daga baya a kara kudin zuwa dala miliyan dubu daya da dubu dari bakwai.
Fadar gwamnatin Zambia a Lusaka, ta na son kara wa’adin yarjejeniyar da ta yi da IMF zuwa karin shekara daya inda ta so ta samu karin dala miliyan 145, kafin daga baya ta sauya ra’ayi, ta zabi ta bari wa’adin ya cika ba tare da ta nemi a kara ba. Ba’a Fadi dalilin yanke wannan hukunci ba.


