A kalla mutane 7 ne suka rasa rayukan su a rikicin da ya barke cikin dare a Uganda bayan gudanar da zaben da ke nuna alamun zarcewar shugaba Yoweri Museveni, a cewar ‘yan sanda ranar Jumu’a.
Sakamakon da hukumar zabe ta sanar ya nuna Museveni na da kashi 75 cikin dari na kuri’un da aka kada ranar Alhamis a Kashi 59 cikin 100 na mazabu, inda babban dan jam’iyyar adawa Bobi Wine kuma ke da kashi 21 cikin dari, sauran kuri’un kuma sun rarrabu tsakanin ‘yan takara 6.
Bayan da yakin neman zabe ya zo da ta tashin hankula a wajajen Taron ‘yan jam’iyyun adawa, da abin da Majalisar Dinkin Duniya ta kira danniya da barazana ga ‘yan adawa, an gudanar da zaben lami lafiya ranar Alhamis.
Amma kuma da daddare sai fada ya kaure a garin Butambala dake da nisan kilomita 55 daga kudu maso gabashin babban birnin kasar na Kampala.
Wani me magana da yawun ‘yan sanda ya ce masu goyon bayan jam’iyyun adawa da wani mamba na majalisa Muwanga Kivumbi ya tara sun far wa tashar ‘yan sandan da adduna, inda ya ce ‘yan sanda sun yi harbi ne don kare kan su, domin mutanen suna da yawa, kuma ya kara da cewa An kama mutane 25


