Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
Published: December 18, 2025 at 10:22 AM | By: Bala Hassan

Najeriya ta yi zargin cewa Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta sanya ‘yan wasa marasa cancanta a gasar cin kofin duniya

Najeriya ta mika takardar koke ga FIFA tana zargin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta sanya ‘yan wasa da basu cancantaba a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta Afirka a shekara mai zuwa, in ji mai magana da yawun hukumar (NFF).

Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo ta doke Najeriya a bugun fenariti a watan da ya gabata don ci gaba da rayuwa a fatanta na fitowa gasar a Arewacin Amurka, kuma za ta fafata a gasar share fagen shiga gasar tsakanin kungiyoyin kwallon kafa a watan Maris inda kungiyoyi shida za su bi sahun matsayi biyu a gasar karshe ta kungiyoyi 48.

NFF ta ce ‘yan wasa da dama ‘yan kasa suna da takardadun izinin kasashe biyu sun bugawa DR Congo wasa ba tare da cika sharuddan da ake bukata ba.

“Dokokin Congo sun ce ba za ka iya samun ‘yan kasa biyu ba,” in ji babban sakataren NFF Mohammed Sanusi ga manema labarai.

“Akwai da yawa daga cikinsu da ke da fasfo na Turai, wasu daga cikinsu fasfo na Faransa, wasu kuma fasfo na Holland.

“Dokokin FIFA sun ce da zarar ka mallaki fasfo na kasarka, ka cancanta.

A ganinmu, sun cancanci hakan ne ya sa FIFA ta wanke su.

“Amma hujjarmu ita ce an yaudari FIFA har ta wanke su domin ba alhakin FIFA ba ne ta tabbatar da cewa an bi ƙa’idodin Congo.”

“FIFA tana bin ƙa’idodinta ne, bisa ga abin da aka gabatar wa FIFA ne ya suka wanke su, mu a wajanmu muna cewa an yi zamba ne.”

 

 

 

 

 

 

 

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kongo ta yi watsi da zarge-zargen da ake ma ta.

“Idan ba za ku iya cin nasara a filin wasa ba, to kada ku yi ƙoƙarin cin nasara daga ƙofar baya,” in ji Hukumar ƙwallon ƙafa ta Kongo (Fecofa) a wani rubutu da ta yi a shafukan sada zumunta.

“Dole ne a buga gasar cin kofin duniya da mutunci da kwarin gwiwa. Ba tare da dabaru na shari’a ba da ku kawo shi.”

FIFA ba ta amsa buƙatar yin tsokaci nan take ba saboda lokutan aiki.

Gasar cin kofin duniya za ta gudana a Amurka, Kanada da Mexico daga 11 ga Yuni zuwa 19 ga Yuli.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC
Next Post: Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika
Ko Arsenal Zata Iya Lashe Gasar Firimiya lig Na Bana Wasanni
‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe
  • Kasar Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Biri
  • Mutane 15 Sun Rasa Rayukan Su A Gabashin Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kwango
  • Kungiyoyi Sunyi Kasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
  • Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai
  • Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup  Wasanni
  • Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Isra’ila Takai Hare Hare Birnin Tehran Afrika
  • CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.