Wani rahoton bayanan leken asiri na Amurka da aka rubuta shi jim kadan kafin Amurka da Isra’ila su far ma kasar Iran da hare-hare, ya cimma daidaito a kan cewa hare-haren sojan Amurka ba zasu iya kawo sauyin shugabanci a kasar ba.
Wasu majiyoyi biyu da suka ga wannan rahoton da hukumomin leken asirin Amurka karkashin inuwar Majalisar Ayyukan Leken Asiri ta kasa suka rubuta a cikin watan Fabrairu, sun ce rahoton ya tsayar da shawarar cewa kai hare-hare ta sama ko kuma jimawa ana kai wadannan hare-haren, zai yi wuya su haifar da sabuwar gwamnati a Iran.
Majiyoyin suka ce rahoton ya ce koda an kashe dukkan shugabannin kasar na yanzu, zai yi wuya a iya canja gwamnatin kasar.
Wannan bayanin, ya gurgunta ikirarin da gwamnatin shugaba Trump take yi cewa zata iya cimma burinta na kai farmakin kan Iran cikin kankanin lokaci.
Mutanen biyu, wadanda suka bukaci da a sakaye sunayensu sun fada ma kamfanin dillancin labaran Associated Press cewa hukumomin leken asirin na Amurka sun cimma daidaito kan cewa babu wasu ‘yan adawa dake da karfi ko hadin kan da zasu iya karbar mulki a kasar Iran ko da an kashe shugabannin kasar.


