Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya
Published: December 5, 2025 at 7:44 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 5, 2025

Shugaba Donald Trump na Amurka ya hada kan shugabannin Kwango ta Kinshasa da Rwanda domin sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya jiya alhamis birnin Washington, duk da cewa har yanzu ana can ana ci gaba da gwabza fada a yankin da ya jima yana fama da fitina.

Shugaba Paul Kagame na Rwanda da shugaba Felix Tshisekedi na Kwango sun rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin kan tattalin arziki da aka cimma a watan da ya shige, da kuma yarjejeniyar zaman lafiyar da Amurka da Qatar suka kulla tsakanin sassan biyu a watan Yuni.

Har ila yau an shirya cewa zasu sanya hannu a kan wata yarjejeniyar game da muhimman ma’adinai.

Rattaba hannu kan yarjejeniyar ta bawa shugaba Donald Trump na Amurka wata sabuwar nasarar da aka ce ba ta zahiri ba, a kokarinsa na nuna cewa shi mai kokarin wanzar da zaman lafiya ne, a wannan karon a saboda har yanzu ana zub da jini a wannan yakin da aka ce an rattaba hannu kan yarjejeniyar kawo karshensa.

Amurka tana kwadayin sanya hannunta a kan ma’adinai masu muhimmanci da yawa da kasar Kwango take da su, kuma tana ta kokarin dakile fintinkau da kasar China ta yi a fannin samo irin wadannan ma’adinai a fadin duniya.

A yayin da shugabannin kasashen biyu ke rattaba hannu a kan wannan yarjejeniya, an bada rahoton gumurzu a tsakanin’yan tawayen kungiyar M23 da Rwanda ke goyon baya da sojojin gwamnatin Kwango a lardin Kivu ta Kudu.

Wani kakakin kungiyar M23 ya zargi sojojin gwamnati da laifin cilla bama bamai a kan yankunan fararen hula.

Masu fashin baki sun ce tsoma bakin Amurka a cikin lamarin ya dakile yaduwar fadan, amma kuma bai iya warware muhimman batutuwan da suka janyo wannan yakin ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili
Next Post: Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
Shirin Kwace Iyakar Greenland Da Shugaba Trump Yakeyi Yabawa Kasashen Turai Mamaki Amurka
Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza Amurka
Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jami’an Shige Da Ficen Amurka Sun Harbe Wani Har Lahira Amurka
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • Da Alamu Ronaldo Zai Buga Dukkan Wasanni Da Gasar Kofin Duniya A 2026 Wasanni
  • Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
  • Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
  • An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
  • An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.